< Job 4 >

1 Then Eliphaz the Temanite replied:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 “If one ventures a word with you, will you be wearied? Yet who can keep from speaking?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Surely you have instructed many, and have strengthened their feeble hands.
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Your words have steadied those who stumbled; you have braced the knees that were buckling.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 But now trouble has come upon you, and you are weary. It strikes you, and you are dismayed.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Is your reverence not your confidence, and the uprightness of your ways your hope?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Consider now, I plead: Who, being innocent, has ever perished? Or where have the upright been destroyed?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 As I have observed, those who plow iniquity and those who sow trouble reap the same.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 By the breath of God they perish, and by the blast of His anger they are consumed.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 The lion may roar, and the fierce lion may growl, yet the teeth of the young lions are broken.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 The old lion perishes for lack of prey, and the cubs of the lioness are scattered.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Now a word came to me secretly; my ears caught a whisper of it.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 In disquieting visions in the night, when deep sleep falls on men,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 fear and trembling came over me and made all my bones shudder.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Then a spirit glided past my face, and the hair on my body bristled.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 It stood still, but I could not discern its appearance; a form loomed before my eyes, and I heard a whispering voice:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 ‘Can a mortal be more righteous than God, or a man more pure than his Maker?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 If God puts no trust in His servants, and He charges His angels with error,
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 how much more those who dwell in houses of clay, whose foundations are in the dust, who can be crushed like a moth!
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 They are smashed to pieces from dawn to dusk; unnoticed, they perish forever.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 Are not their tent cords pulled up, so that they die without wisdom?’
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >