< Job 26 >

1 Then Job answered:
Sai Ayuba ya amsa,
2 “How you have helped the powerless and saved the arm that is feeble!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 How you have counseled the unwise and provided fully sound insight!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 To whom have you uttered these words? And whose spirit spoke through you?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 The dead tremble— those beneath the waters and those who dwell in them.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Sheol is naked before God, and Abaddon has no covering. (Sheol h7585)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
7 He stretches out the north over empty space; He hangs the earth upon nothing.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 He wraps up the waters in His clouds, yet the clouds do not burst under their own weight.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 He covers the face of the full moon, spreading over it His cloud.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 He has inscribed a horizon on the face of the waters at the boundary between light and darkness.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 The foundations of heaven quake, astounded at His rebuke.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 By His power He stirred the sea; by His understanding He shattered Rahab.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 By His breath the skies were cleared; His hand pierced the fleeing serpent.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Indeed, these are but the fringes of His ways; how faint is the whisper we hear of Him! Who then can understand the thunder of His power?”
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”

< Job 26 >