< Job 17 >

1 “My spirit is broken; my days are extinguished; the grave awaits me.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Surely mockers surround me, and my eyes must gaze at their rebellion.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 Give me, I pray, the pledge You demand. Who else will be my guarantor?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 You have closed their minds to understanding; therefore You will not exalt them.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 If a man denounces his friends for a price, the eyes of his children will fail.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 He has made me a byword among the people, a man in whose face they spit.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 My eyes have grown dim with grief, and my whole body is but a shadow.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 The upright are appalled at this, and the innocent are stirred against the godless.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 Yet a righteous one holds to his way, and the one with clean hands grows stronger.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 But come back and try again, all of you. For I will not find a wise man among you.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 My days have passed; my plans are broken off— even the desires of my heart.
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 They have turned night into day, making light seem near in the face of darkness.
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 If I look for Sheol as my home, if I spread out my bed in darkness, (Sheol h7585)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
14 and say to corruption, ‘You are my father,’ and to the worm, ‘My mother,’ or ‘My sister,’
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 where then is my hope? Who can see any hope for me?
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 Will it go down to the gates of Sheol? Will we go down together into the dust?” (Sheol h7585)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)

< Job 17 >