< Jeremiah 47 >

1 This is the word of the LORD that came to Jeremiah the prophet about the Philistines before Pharaoh struck down Gaza.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
2 This is what the LORD says: “See how the waters are rising from the north and becoming an overflowing torrent. They will overflow the land and its fullness, the cities and their inhabitants. The people will cry out, and all who dwell in the land will wail
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
3 at the sound of the galloping hooves of stallions, the rumbling of chariots, and the clatter of their wheels. The fathers will not turn back for their sons; their hands will hang limp.
da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
4 For the day has come to destroy all the Philistines, to cut off from Tyre and Sidon every remaining ally. Indeed, the LORD is about to destroy the Philistines, the remnant from the coasts of Caphtor.
Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
5 The people of Gaza will shave their heads in mourning; Ashkelon will be silenced. O remnant of their valley, how long will you gash yourself?
Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
6 ‘Alas, O sword of the LORD, how long until you rest? Return to your sheath; cease and be still!’
“Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
7 How can it rest when the LORD has commanded it? He has appointed it against Ashkelon and the shore of its coastland.”
Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”

< Jeremiah 47 >