< Hebrews 3 >

1 Therefore, holy brothers, who share in the heavenly calling, set your focus on Jesus, the apostle and high priest whom we confess.
Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
2 He was faithful to the One who appointed Him, just as Moses was faithful in all God’s house.
Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
3 For Jesus has been counted worthy of greater glory than Moses, just as the builder of a house has greater honor than the house itself.
An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
4 And every house is built by someone, but God is the builder of everything.
Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
5 Now Moses was faithful as a servant in all God’s house, testifying to what would be spoken later.
Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
6 But Christ is faithful as the Son over God’s house. And we are His house, if we hold firmly to our confidence and the hope of which we boast.
Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
7 Therefore, as the Holy Spirit says: “Today, if you hear His voice,
Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
8 do not harden your hearts, as you did in the rebellion, in the day of testing in the wilderness,
kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
9 where your fathers tested and tried Me, and for forty years saw My works.
inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
10 Therefore I was angry with that generation, and I said, ‘Their hearts are always going astray, and they have not known My ways.’
Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
11 So I swore on oath in My anger, ‘They shall never enter My rest.’”
Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
12 See to it, brothers, that none of you has a wicked heart of unbelief that turns away from the living God.
Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
13 But exhort one another daily, as long as it is called today, so that none of you may be hardened by sin’s deceitfulness.
Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
14 We have come to share in Christ if we hold firmly to the end the assurance we had at first.
Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
15 As it has been said: “Today, if you hear His voice, do not harden your hearts, as you did in the rebellion.”
Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
16 For who were the ones who heard and rebelled? Were they not all those Moses led out of Egypt?
Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
17 And with whom was God angry for forty years? Was it not with those who sinned, whose bodies fell in the wilderness?
Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
18 And to whom did He swear that they would never enter His rest? Was it not to those who disobeyed?
Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
19 So we see that it was because of their unbelief that they were unable to enter.
Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.

< Hebrews 3 >