< Ecclesiastes 1 >

1 These are the words of the Teacher, the son of David, king in Jerusalem:
Kalmomin Malami, ɗan Dawuda, Sarki a Urushalima.
2 “Futility of futilities,” says the Teacher, “futility of futilities! Everything is futile!”
“Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami. “Gaba ɗaya ba amfani! Kome ba shi da amfani!”
3 What does a man gain from all his labor, at which he toils under the sun?
Wace riba ce mutum yake samu daga wahalar da yake fama a duniya?
4 Generations come and generations go, but the earth remains forever.
Zamanai sukan zo zamanai su wuce, amma duniya tana nan har abada.
5 The sun rises and the sun sets; it hurries back to where it rises.
Rana takan fito rana ta kuma fāɗi, ta kuma gaggauta zuwa inda takan fito.
6 The wind blows southward, then turns northward; round and round it swirls, ever returning on its course.
Iska takan hura zuwa kudu ta kuma juya zuwa arewa; tă yi ta kewayewa, tă yi ta koma inda take fitowa.
7 All the rivers flow into the sea, yet the sea is never full; to the place from which the streams come, there again they flow.
Dukan rafuffuka sukan gangara zuwa teku, duk da haka teku ba ya cika. Daga inda rafuffukan suke fitowa, a can suke komawa kuma.
8 All things are wearisome, more than one can describe; the eye is not satisfied with seeing, nor the ear content with hearing.
Dukan abubuwa suna kawo gajiya, gaban magana. Ido ba ya gaji da gani, haka ma kunne yă ƙoshi da ji.
9 What has been will be again, and what has been done will be done again; there is nothing new under the sun.
Abin da ya taɓa kasancewa, zai sāke kasance, abin da aka yi za a sāke yi kuma; babu wani abu sabo a duniya.
10 Is there a case where one can say, “Look, this is new”? It has already existed in the ages before us.
Akwai wani abin da za a ce, “Duba! Ga wani abu sabo”? Abin yana nan, tun dā can, ya kasance kafin lokacinmu.
11 There is no remembrance of those who came before, and those yet to come will not be remembered by those who follow after.
Ba a tunawa da mutanen dā, haka su ma da ba a haifa ba tukuna waɗanda za su biyo bayansu ba za a tuna da su ba.
12 I, the Teacher, was king over Israel in Jerusalem.
Ni, Malami, sarki ne bisa Isra’ila a Urushalima.
13 And I set my mind to seek and explore by wisdom all that is done under heaven. What a heavy burden God has laid upon the sons of men to occupy them!
Na dauri aniyata in gwada don in bincika ta wurin hikima dukan abin da ake yi a duniya. Kaya mai nauyi ne Allah ya ɗora a kan mutane!
14 I have seen all the things that are done under the sun, and have found them all to be futile, a pursuit of the wind.
Na ga dukan abubuwan da ake yi a duniya, dukansu ba su da amfani, naushin iska ne kawai.
15 What is crooked cannot be straightened, and what is lacking cannot be counted.
Abin da yake tanƙwararre ba zai miƙu ba; ba za a kuma iya ƙidaya abin da ba shi ba.
16 I said to myself, “Behold, I have grown and increased in wisdom beyond all those before me who were over Jerusalem, and my mind has observed a wealth of wisdom and knowledge.”
Na yi tunani a raina na ce, “Duba, na yi girma, na kuma ƙaru da hikima fiye da duk wanda ya taɓa mulki a bisa Urushalima kafin ni; na ɗanɗana hikima mai yawa da kuma ilimi.”
17 So I set my mind to know wisdom and madness and folly; I learned that this, too, is a pursuit of the wind.
Sa’an nan na ɗaura aniyata ga fahimtar hikima, in kuma san bambanci tsakanin hauka da wauta, amma na koyi cewa wannan ma, naushin iska ne kawai.
18 For with much wisdom comes much sorrow, and as knowledge grows, grief increases.
Gama yawan hikima yakan kawo yawan baƙin ciki; yawan sani, yawan ɓacin rai.

< Ecclesiastes 1 >