< 2 Samuel 22 >

1 And David sang this song to the LORD on the day the LORD had delivered him from the hand of all his enemies and from the hand of Saul.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 He said: “The LORD is my rock, my fortress, and my deliverer.
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 My God is my rock, in whom I take refuge, my shield, and the horn of my salvation. My stronghold, my refuge, and my Savior, You save me from violence.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 I will call upon the LORD, who is worthy to be praised; so shall I be saved from my enemies.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 For the waves of death engulfed me; the torrents of chaos overwhelmed me.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 The cords of Sheol entangled me; the snares of death confronted me. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
7 In my distress I called upon the LORD; I cried out to my God. And from His temple He heard my voice, and my cry for help reached His ears.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Then the earth shook and quaked; the foundations of the heavens trembled; they were shaken because He burned with anger.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Smoke rose from His nostrils, and consuming fire came from His mouth; glowing coals blazed forth.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 He parted the heavens and came down with dark clouds beneath His feet.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 He mounted a cherub and flew; He soared on the wings of the wind.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 He made darkness a canopy around Him, a gathering of water and thick clouds.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 From the brightness of His presence coals of fire blazed forth.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 The LORD thundered from heaven; the voice of the Most High resounded.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 He shot His arrows and scattered the foes; He hurled lightning and routed them.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 The channels of the sea appeared, and the foundations of the world were exposed at the rebuke of the LORD, at the blast of the breath of His nostrils.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 He reached down from on high and took hold of me; He drew me out of deep waters.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 He rescued me from my powerful enemy, from foes too mighty for me.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 They confronted me in my day of calamity, but the LORD was my support.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 He brought me out into the open; He rescued me because He delighted in me.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 The LORD has rewarded me according to my righteousness; He has repaid me according to the cleanness of my hands.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 For I have kept the ways of the LORD and have not wickedly departed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 For all His ordinances are before me; I have not disregarded His statutes.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 And I have been blameless before Him and kept myself from iniquity.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 So the LORD has repaid me according to my righteousness, according to my cleanness in His sight.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 To the faithful You show Yourself faithful, to the blameless You show Yourself blameless;
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 to the pure You show Yourself pure, but to the crooked You show Yourself shrewd.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 You save an afflicted people, but Your eyes are on the haughty to bring them down.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 For You, O LORD, are my lamp; the LORD lights up my darkness.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 For in You I can charge an army; with my God I can scale a wall.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 As for God, His way is perfect; the word of the LORD is flawless. He is a shield to all who take refuge in Him.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 For who is God besides the LORD? And who is the Rock except our God?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 God is my strong fortress and He makes my way clear.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 He makes my feet like those of a deer and stations me upon the heights.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 He trains my hands for battle; my arms can bend a bow of bronze.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 You have given me Your shield of salvation, and Your gentleness exalts me.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 You broaden the path beneath me so that my ankles do not give way.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 I pursued my enemies and destroyed them; I did not turn back until they were consumed.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 I devoured and crushed them so they could not rise; they have fallen under my feet.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 You have armed me with strength for battle; You have subdued my foes beneath me.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 You have made my enemies retreat before me; I put an end to those who hated me.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 They looked, but there was no one to save them— to the LORD, but He did not answer.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 I ground them as the dust of the earth; I crushed and trampled them like mud in the streets.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 You have delivered me from the strife of my people; You have preserved me as the head of nations; a people I had not known shall serve me.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Foreigners cower before me; when they hear me, they obey me.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Foreigners lose heart and come trembling from their strongholds.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 The LORD lives, and blessed be my Rock! And may God, the Rock of my salvation, be exalted—
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 the God who avenges me and brings down nations beneath me,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 who frees me from my enemies. You exalt me above my foes; You rescue me from violent men.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Therefore I will praise You, O LORD, among the nations; I will sing praises to Your name.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 Great salvation He brings to His king. He shows loving devotion to His anointed, to David and his descendants forever.”
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

< 2 Samuel 22 >