< 1 Timothy 2 >
1 First of all, then, I urge that petitions, prayers, intercessions, and thanksgiving be offered for everyone—
Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
2 for kings and all those in authority—so that we may lead tranquil and quiet lives in all godliness and dignity.
da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
3 This is good and pleasing in the sight of God our Savior,
Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
4 who wants everyone to be saved and to come to the knowledge of the truth.
wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
5 For there is one God, and there is one mediator between God and men, the man Christ Jesus,
Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
6 who gave Himself as a ransom for all—the testimony that was given at just the right time.
wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
7 For this reason I was appointed as a preacher, an apostle, and a faithful and true teacher of the Gentiles. I am telling the truth; I am not lying about anything.
Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
8 Therefore I want the men everywhere to pray, lifting up holy hands, without anger or dissension.
Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
9 Likewise, I want the women to adorn themselves with respectable apparel, with modesty, and with self-control, not with braided hair or gold or pearls or expensive clothes,
Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
10 but with good deeds, as is proper for women who profess to worship God.
sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
11 A woman must learn in quietness and full submissiveness.
Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
12 I do not permit a woman to teach or to exercise authority over a man; she is to remain quiet.
Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
13 For Adam was formed first, and then Eve.
Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
14 And it was not Adam who was deceived, but the woman who was deceived and fell into transgression.
Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
15 Women, however, will be saved through childbearing, if they continue in faith, love, and holiness, with self-control.
Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.