< Romans 2 >

1 For which reason, you are without excuse, O man, whoever you are, that judge; for in that in which you judge another, you condemn yourself; for you who judge, practice the same things.
Saboda da haka baka da hujja, kai mutum, kai mai shara'antawa, domin kuwa abinda kake shara'antawa akan wasu kana kada kanka da kanka. Domin kuwa kai mai shar'antaawa kana aikata wadannan abubuwa.
2 But we know that the judgment of God against those who practice such things, is according to truth.
Amma mun san cewa shari'ar Allah ta gaskiya ce sa'adda zata fado wa masu aikata wadannan irin abubuwa.
3 But do you, O man, who judge those that practice such things, and yet do the same, conclude that you will escape the judgment of God?
Amma ka lura da wannan, ya kai mutum, mai shara'anta masu aikata wadannan ababuwa. Duk da shike kaima kana aikatawa. Kana jin zaka kubucewa hukuncin Allah?
4 Or, do you despise the riches of his goodness, and his forbearance, and his long suffering, not knowing that the goodness of God leads you to repentance?
Ko kana raina falalar alheransa da yake yi ta wajen jinkirin hukuncinsa, da hakurinsa? Baka san cewa alheransa musanman domin su kai ka ga tuba bane?
5 But, according to your hard and impenitent heart, you treasure up to yourself wrath for a day of wrath, and of the revelation of the righteous judgment of God,
Amma saboda taurin kanka da zuciyarka marar tuba, kana tanadarwa kanka fushi, a ranar fushi, wato ranar bayyanuwar shari'ar adalci ta Allah.
6 who will render to every man according to his works;
Zai baiwa kowanne mutum daidai sakamakon ayyukansa:
7 to those who, by patient continuance in good works, seek for glory and honor and incorruptibility, eternal life: (aiōnios g166)
Ga wadanda kuma suka nace da yin ayyukan alheri ba fasawa, sun samarwa kansu, yabo da daraja, da rai na har'abada. (aiōnios g166)
8 but to those who are contentious, and obey not the truth, but obey unrighteousness, anger and wrath,
Amma ga masu son kai, wadanda suka ki yin biyayya ga gaskiya, suka yiwa rashin adalci biyayya, fushi da hasala mai zafi zai afko masu.
9 affliction and distress, upon every soul of man that practices what is evil, of the Jew first, and also of the Greek:
Allah kuma zai sauko da bala'i da bakin ciki ga dukkan rayukan da suka aikata mugunta, ga Yahudawa da fari, sannan kuma Hellinawa.
10 but glory and honor and peace to every one that practices what is good, to the Jew first, and also to the Greek:
Amma yabo daraja da salama zasu kasance ga dukkan wadanda suka aikata ayukan alheri, ga Yahudawa da fari sannan Hellanawa.
11 for there is no respect of persons with God.
Domin kuwa Allah ba mai tara bane.
12 For as many as have sinned without law, shall also perish without law; and as many as have sinned under law, shall be judged by law,
Ga wadanda suka yi zunubi batare da shari'aba, zasu hallaka ba tare da shari'a ba, ga wadanda suka yi zunubi cikin shari'a kuma za'a hukunta su bisa ga shari'a.
13 in the day when God shall judge the secret works of men by Jesus Christ, according to my gospel.
Domin kuwa ba masu jin shari'ar ne masu adalci agaban Allah ba, amma masu aikatawa ne zasu samu barata.
14 For not the hearers of the law are just before God, but the doers of the law shall be justified.
Gama al'umai da basu san shari'a ba, bisa ga dabi'a sun yi abinda ke na shari'a, sun kuma zame wa kansu shari'a, koda shike basu da shari'ar.
15 For when the Gentiles, who have not a law, do, by nature, the things of the law, these who have not a law, are a law to themselves,
Dalilin haka kuwa sun nuna cewa ayukan da shari'a take bukata na nan a rubuce a zuciyarsu. lamirinsu kuma na yi masu shaida, tunanainsu kuma, ko dai yana kashe su, ko kuma yana karesu.
16 who show that the work which the law requires, is written in their hearts, their conscience bearing testimony, and their reasonings with each other accusing, or making excuse.
hakanan kuma ga Allah. Wannan zai faru ranar da Allah zai shara'anta asiran boye na dukkan mutane, bisa ga bishara ta cikin Yesu Almasihu.
17 But if you are named Jew, and rest in the law, and make your boast in God.
Da shike kana kiran kanka Bayahude, kana zaune akan shari'a, kana alfahari cikin Allah,
18 and know his will, and approve what is excellent, being instructed by the law:
ka san nufinsa, ka kuma san abubuwan da suka bambanta da hakan, ka kuma sami koyarwa cikin shari'ar.
19 if you are also confident that you yourself are a guide for the blind, a light to those who are in darkness,
Da shike kana da gabagadi akan cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga wadanda suke cikin duhu,
20 an instructor of the simple, a teacher of the unlearned, because you have the form of true knowledge in the law;
mai horo ga marasa hikima, mai koyar da jarirai, kuma a cikin shari'ar kana da abin da ya shafi sani da kuma gaskiya.
21 you, then, who teach another, do you not teach yourself? You who preach that a man should not steal, do you steal?
ku da kuke koyar da wadansu, ba ku koyar da kanku? ku da kuke wa'azi kada ayi sata, ba ku yin sata?
22 You who say that a man should not commit adultery, do you commit adultery? You who detest idols, do you rob temples?
Ku da ke wa'azi kada ayi zina, ba ku yin zina? ku da ke hana bautar gumaka, ba ku yin sata a haikali?
23 You who make your boast in the law, do you, by transgressing the law, dishonor God?
ku masu murna da tinkaho cikin shari'ar, ba kwa wulakanta Allah cikin kurakuranku na rashin bin shari'a?
24 For the name of God is reviled among the Gentiles, on account of you, as it is written.
''Domin kuwa an wulakanta sunan Allah cikin Al'umai sabili da ku,'' kamar yadda aka riga aka rubuta.
25 Now, circumcision is indeed profitable, if you keep the law: but, if you transgress the law, your circumcision becomes uncircumcision.
Lallai kuwa kaciya tana da riba a gare ku, idan kuka kiyaye doka, amma idan ku marasa bin doka ne kaciyarku ta zama rashin kaciya.
26 If, then, he who is uncircumcised keeps the righteousness of the law, shall not his uncircumcision be counted for circumcision?
domin kuwa idan mutum marar kaciya zai kiyaye dukkan bukatun doka, baza'a iya daukan rashin kaciyarsa a matsayin mai kaciya ba?
27 And shall not he whose want of circumcision is owing to his birth, if he keeps the law, condemn you, who, by the literal circumcision, transgress the law?
Sannan idan mutum marar kaciya ta jini zai kiyaye dukkan dokoki, ba zai iya shara'anta ku masu kaciya ta shari'a ba? Haka kuma ya kasance ne domin kuna da shari'a a rubuce da kuma kaciya amma ba kwa bin doka!
28 For he is not a Jew who is one outwardly, nor is that circumcision which is outward in the flesh:
Domin shi kuwa ba Bayahude bane a waje; ba kuwa mai kaciyar da aka tsaga fata ba.
29 but he is a Jew who is one inwardly; and circumcision is that of the heart, in the spirit, not in the letter, whose praise is not of men, but of God.
Amma Bayahude ne ta ciki, sanna kuma mai kaciyar zuciya da kuma ruhu ba wasika ba, irin wanna mutumin yabonsa ba daga wurin mutane yake zuwa ba, amma daga Allah.

< Romans 2 >