< Mark 4 >
1 And again he began to teach by the sea; and a great multitude came together to him, so that he went into a ship, and sat in the sea: and the whole multitude was on the land near the sea.
Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
2 And he taught them many things in parables, and said to them in his teaching:
Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
3 Hear; Behold, the sower went forth to sow;
“Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
4 and it came to pass, as he sowed, that some seed fell by the wayside, and the birds came and ate it up.
Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
5 Other seed fell on stony ground, where it had not much earth: and it immediately sprung up, because it had no depth of earth.
Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
6 And when the sun was up, it was scorched; and because it had no root, it withered away.
Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
7 And other seed fell among thorns, and the thorns grew up and choked it, and it produced no fruit.
Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
8 And other seed fell in the good ground, and produced fruit that grew up and increased, and produced, one thirty, one sixty, and one a hundred.
Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
9 And he said: He that has ears to hear, let him hear.
Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
10 And when he was alone, those who were about him, with the twelve, asked him the meaning of the parable.
Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
11 And he said to them: To you it is given to know the mystery of the kingdom of God; but to those who are without, all things are done in parables;
Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
12 that they may surely see, and not perceive; and that they may surely hear, and not understand; lest they should turn to me, and their sins should be forgiven them.
Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
13 And he said to them: Do you not understand this parable? And how then will you understand all parables?
Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
14 The sower sows the word.
Manomi yakan shuka maganar Allah.
15 These are they that received seed by the wayside, where the word is sown; and when they hear, Satan immediately comes and takes away the word that was sown in their hearts.
Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
16 And these are they that, in like manner, received seed in stony places: who, when they hear the word, immediately receive it with joy:
Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
17 and they have no root in themselves, but endure for a time; afterward, when affliction or persecution arises on account of the word, they immediately take offense.
Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
18 And these are they that received seed among thorns; who hear the word,
Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
19 and the anxieties of this age, and the deceitfulness of riches, and desires for other things enter in and choke the word, and it becomes unfruitful. (aiōn )
amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
20 And these are they that received seed on the good ground; who hear the word, and receive it, and bring forth fruit, one thirty, and one sixty, and one a hundred.
Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
21 And he said to them: Is a lamp brought in that it may be put under the measure, or under the divan? Is it not brought that it may be put on the lamp-stand?
Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
22 For there is nothing hid that shall not be made known; nor has any thing been concealed, but that it may come into open view.
Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
23 If any one has ears to hear, let him hear.
Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
24 And he said to them: Take heed how you hear; with what measure you measure, it shall be measured to you; and to you that hear, more shall be given;
Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
25 for whoever has, to him shall be given; and whoever has not, even that which he has shall be taken from him.
Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
26 And he said: So is the kingdom of God, as if a man should sow seed in the ground,
Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
27 and should sleep and rise, night and day, and the seed should spring up and grow, he knows not how.
A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
28 For the earth, of its own accord, produces fruit, first the blade; then the ear, then the full grain in the ear.
Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
29 But when the fruit is ripe, immediately he sends forth the sickle, because the harvest is ready.
Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
30 And he said: To what shall we liken the kingdom of God? Or, by what similitude shall we illustrate it?
Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
31 It is like a grain of mustard, which, when it is sown in the ground, is less than all seeds that are in the ground;
Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
32 yet, when it is sown, it grows up, and becomes larger than all garden-plants, and sends out great branches, so that the birds of the air can roost under its shadow.
Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
33 And with many such parables he spoke the word to them, as they were able to hear.
Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
34 But without a parable he did not speak to them; but when alone, he explained all things to his disciples.
Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
35 And on the same day, when it was evening, he said to them: Let us go over to the opposite side.
A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
36 And when they had sent the multitude away, they took him with them, as he was in the ship; and there were other little ships with him.
Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
37 And there arose a great storm of wind, and the waves dashed into the ship, so that it was now full.
Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
38 And he was in the hinder part of the ship, asleep on the pillow. And they awoke him, and said to him: Teacher, carest thou not that we perish?
Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
39 And he arose, and rebuked the wind, and said to the sea: Peace, be still. And the wind ceased, and there was a great calm.
Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
40 And he said to them: Why are you so fearful? How is it that you have no faith?
Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
41 And they were greatly afraid, and said one to another: Who, then, is this, that even the wind and the sea obey him?
Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”