< John 1 >

1 In the beginning was the WORD, and the WORD was with God, and the WORD was God.
A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
2 He was in the beginning with God.
Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
3 All things were made by him, and without him not one thing was made that now exists.
Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
4 In him was life, and the life was the light of men.
A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
5 And the light shines in the darkness, and the darkness comprehends it not.
Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6 There was a man sent from God, whose name was John.
Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 This man came as a witness, to testify of the Light, that all through him might believe.
Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
8 He was not the Light; but he came to testify of the Light.
Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9 He was the true Light, which, coming into the world, gives light to every man.
Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10 He was in the world, and the world was made by him, and the world knew him not.
Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
11 He came to his own country, and his own people received him not.
Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12 But as many as received him, to them he gave the privilege of becoming the children of God, even to those who believe on his name;
Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
13 who were begotten, not of blood, nor of the will of the flesh, nor of the will of man, but of God.
Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14 And the WORD became flesh, and tabernacled among us, (and we beheld his glory, the glory as of the only begotten of the Father, ) full of grace and of truth.
Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
15 John testified of him, and cried, saying: This is he of whom I said: He that comes after me, is now before me, for he existed before me.
Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
16 And from his fullness have we all received, even grace for grace;
Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
17 for the law was given through Moses, but the grace and the truth came through Jesus Christ.
Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
18 No one has seen God at any time; the only begotten Son, who is in the bosom of the Father, he has revealed him.
Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19 And this is the testimony of John, when the Jews sent priests and Levites from Jerusalem to ask him: Who are you?
Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
20 And he confessed, and did not deny; and he confessed: I am not the Christ.
Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
21 And they asked him: What then? Are you Elijah? And he said: I am not. Are you the prophet? And he answered: No.
Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
22 They then said to him: Who are you? that we may give an answer to those who sent us; what say you of yourself?
Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
23 He said: I am the voice of one crying in the wilderness, Make straight the way of the Lord; as said the prophet Isaiah.
Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
24 And those who were sent were of the Pharisees;
Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
25 and they asked him, and said to him: Why, then, do you immerse, if you are not the Christ, nor Elijah, nor the prophet?
“To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
26 John answered them, saying: I immerse in water; but there stands one among you whom you know not.
Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
27 He it is, who, though he comes after me, is now before me; the strap of whose sandal I am not worthy to loose.
shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
28 These things were done in Bethany, beyond the Jordan, where John was immersing.
Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29 The next day John saw Jesus coming to him, and said: Behold the Lamb of God, that takes away the sin of the world.
Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
30 This is he of whom I said, After me comes a man who is now before me, for he existed before me.
Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
31 And I knew him not; but that he might be made manifest to Israel, for this reason I have come immersing in water.
Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
32 And John testified, saying: I saw the Spirit descending from heaven like a dove, and it remained on him.
Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
33 And I knew him not; but he that sent me to immerse in water, said to me, On whom you shall see the Spirit descending and remaining, this is he that immerses in the Holy Spirit.
Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
34 And I saw, and do testify that this is the Son of God.
Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
35 Again the next day, John was standing with two of his disciples.
Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
36 And looking on Jesus as he walked, he said: Behold the Lamb of God.
suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
37 And the two disciples heard him speak, and they followed Jesus.
Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
38 And Jesus turned, and saw them following, and said to them:
Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
39 What do you seek? They said to him: Rabbi, (which, when translated, is called Teacher, ) where abidest thou?
Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40 He said to them: Come and see. They went and saw where he abode; and they remained with him that day; for it was about the tenth hour.
Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
41 One of the two that heard John speak, and followed him, was Andrew, the brother of Simon Peter.
Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
42 He first found his own brother Simon, and said to him: We have found the Messiah; (which, when translated, is the Christ; )
Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
43 and he brought him to Jesus. Jesus looking on him, said: You are Simon, the son of Jonah; you shall be called Cephas (which, when translated, is Rock).
Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
44 The day following, Jesus wished to go into Galilee; and he found Philip, and said to him: Follow me.
Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
45 Now, Philip was of Bethsaida, the city of Andrew and Peter.
Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
46 Philip found Nathaniel, and said to him: We have found him of whom Moses in the law and the prophets did write, Jesus of Nazareth, the son of Joseph.
Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
47 And Nathaniel said to him: Can any thing good come out of Nazareth? Philip said to him: Come and see.
Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
48 Jesus saw Nathaniel coming to him, and said of him: Be hold, an Israelite in truth, in whom there is no guile.
Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
49 Nathaniel said to him: How knowest thou me? Jesus answered and said to him: Before Philip called you, while you were under the fig-tree, I saw you.
Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
50 Nathaniel answered and said to him: Rabbi, thou art the Son of God; thou art the King of Israel.
Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
51 Jesus answered and said to him: Do you believe, because I said to you, I saw you under the fig-tree? You shall see greater things than these. And he said to him: Verily, verily I say to you, From this time you shall see heaven opened, and the angels of God ascending and descending upon the Son of man.
Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”

< John 1 >