< Acts 13 >
1 Now there were certain prophets and teachers in the church that was at Antioch; Barnabas, and Simeon, who is called Niger, and Lucius of Cyrene, and Manaen, who was brought up with Herod the tetrarch, and Saul.
A cikin iklisiyar da take Antakiya, akwai annabawa da malamai. Sune su Barnabas, Saminu (wadda ake kira Baki) da Lukiya Bakurame da Manayin (wanda aka yi renon su tare da sarki Hiridus mai mulki) da Shawulu.
2 And while they were ministering to the Lord, and fasting, the Holy Spirit said: Set apart for me Barnabas and Saul, to the work to which I have called them.
Sa'adda suke bauta wa Allah tare da azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ku kebe mani Barnaba da Shawulu domin aikin da na kiraye su”.
3 Then, after they had fasted and prayed, and laid their hands on them, they sent them away.
Bayan taron sun yi addu'a da azumi, sai suka sa masu hannu, su suka sallame su.
4 Therefore, having been sent forth by the Holy Spirit, they went down to Seleucia, and thence sailed to Cyprus.
Sai Shawulu da Barnabas suka yi biyayya da Ruhu Mai Tsarki suka tafi Sulukiya; daga nan suka ketare zuwa tsibirin Kuburus.
5 And while they were in Salamis, they preached the word of God in the synagogue of the Jews; and they had John as their attendant.
Sa'adda suke garin Salami, suka koyar da maganar Ubangiji a majami'un Yahudawa, suna kuma tare da Yahaya Markus mai taimakonsu.
6 And having gone through the island as far as Paphos, they found a certain magician, a Jewish false prophet, whose name was Bar-jesus;
Bayan sun zaga tsibirin duka har Bafusa, nan suka iske wani Bayahude mai suna Bar-yeshua mai tsafi kuma annabin karya.
7 and he was with the proconsul, Sergius Paulus, who was a man of intelligence. This man called for Barnabas and Saul, and expressed an earnest wish to hear the word of God.
Wannan mai tsafin wanda ke tare da Makaddas, shi Sarjus Bulus mutum mai basira ne. Wannan kuwa ya kira Shawulu da Barnaba domin yana so ya ji maganar Allah.
8 But the magician Elymas (for this is his name, when translated) withstood them, desiring to turn away the proconsul from the faith.
Amma Elimas “mai tsafi” (fasarar sunansa kenan) ya yi adawa da su; yana so ya baudar da Makaddashin daga bangaskiya.
9 Then Saul, who is also called Paul, filled with the Holy Spirit, and looking earnestly upon him,
Amma Shawulu wanda ake ce da shi Bulus yana cike da Ruhu Mai Tsarki ya kafa masa ido.
10 said: O full of all deceit and all wickedness, child of the devil, enemy of all righteousness, will you not cease to pervert the right ways of the Lord?
Sai ya ce, “Kai dan iblis, kana cike da kowace irin yaudara da mugunta. Kai abokin gabar kowanne irin adalci ne. Ba za ka daina karkata mikakkakun hanyoyin Ubangiji ba?
11 And now, behold, the hand of the Lord is upon you, and you shall be blind, not seeing the sun for a season. And immediately there fell on him a mist and a darkness, and he went about and sought some to lead him by the hand.
Yanzu ga hannun Ubangiji bisa kanka, zaka zama makaho. Ba za ka ga rana ba nan da dan lokaci.” Nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi ya fara yawo yana neman mutane su yi masa jagora.
12 Then the proconsul, seeing what was done, believed, being amazed at the teaching of the Lord.
Bayan da Makaddashin ya ga abin da ya faru ya ba da gaskiya saboda ya yi mamakin koyarwa game da Ubangiji.
13 And Paul and his companions put to sea from Paphos, and went to Perga in Pamphylia. But John withdrew from them, and returned to Jerusalem.
Bulus da abokansa suka shirya suka ketare a jirgin ruwa daga Bafusa zuwa Firjiya a Bamfiliya. Amma Yahaya ya bar su ya koma Urushalima.
14 But having passed through from Perga, they came to Antioch in Pisidia; and on the sabbath-day they went into the synagogue, and sat down.
Bulus da abokansa suka tafi daga Firjiya zuwa Antakiya na kasar Bisidiya. Nan suka shiga majami'a ran Asabaci suka zauna.
15 After the reading of the law and the prophets, the rulers of the synagogue sent to them, saying: Brethren, if you have a word of exhortation for the people, speak.
Bayan karatun dokoki da annabawa, shugabanin iklisiyar suka tura sako cewa, “'Yan'uwa, idan kuna da wani sakon karfafawa ga jama'a ku fadi.”
16 Then Paul arose, and waving his hand, said: Men of Israel, and you who fear God, give audience.
Bulus kuwa ya tashi ya yi alama da hannunsa ya ce, “Mutanen Isra'ila da ku wadanda kuke girmama Allah, ku ji.
17 The God of this people chose our fathers, and exalted the people when they sojourned in the land of Egypt, and with an uplifted arm he brought them out from it.
Allahn Isar'ila ya zabi kakkaninmu ya kuma ribabbanya su sa'adda suke kasar Masar da kuma madaukakin iko ya fito da su daga cikinta.
18 And for about forty years, he cherished them in the wilderness.
Ya yi hakuri da su a jeji har na tsawon shekara arba'in.
19 And when he had destroyed seven nations in the land of Chanaan, he divided their land among them by lot.
Bayan ya hallaka kasashe bakwai a kasar Kan'ana, ya ba kakkaninmu kasar nan gado.
20 And after that he gave them judges, for about four hundred and fifty years, till Samuel the prophet.
Duk wadanan abubuwan sun faru shekaru dari hudu da hamsin da suka wuce. Bayan wadannan, Allah ya ba su alkalai har sai da annabi Sama'ila ya zo.
21 And afterward they asked for a king, and God gave them Saul the son of Kis, a man of the tribe of Benjamin, for forty years.
Sai jama'a suka roka a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Saul dan Kish, mutumin kabilar Binyamin ya zama sarki har na tsawon shekara arba'in.
22 And when he had removed him, he raised up David to be their king; to whom he gave this testimony: I have found David the son of Jesse a man after my own heart, who will do all my will.
Allah kuwa ya cire shi daga kan kujerar sarauta, ya daga Dauda ya zama sarkinsu. A kan Dauda ne Allah ya ce, 'Na sami Dauda dan Yessi, mutumin da zuciyata ke so; zai yi duk abin da nake so'.
23 From the posterity of this man, God, according to his promise, raised up for Israel a Savior, Jesus;
Daga zuriyar mutumin nan Allah ya fito da mai ceto, Yesu, kamar yadda aka alkawarta zai yi.
24 John having first preached, before his coming, the immersion of repentance to all the people of Israel.
Wannan ya faru kafin Yesu ya zo, Yahaya ya yi shelar baftimar tuba ga jamma'ar Isra'ila.
25 And as John was finishing his course, he said: Who do you suppose that I am? I am not he; but behold, there is coming after me one, the sandals of whose feet I am not worthy to loose.
Sa'adda Yahaya ya gama aikin sa, sai ya ce, 'Wanene ni a tsamanin ku? Ba nine shi ba. Amma ku saurara, akwai wani mai zuwa bayana wanda maballin takalminsa ban isa in kwance ba.'
26 Brethren, sons of the family of Abraham, and those among you who fear God, to you is the word of this salvation sent.
Yan'uwa 'ya'ya daga zuriyar Ibrahim, da wadanda ke bautar Allah a cikinku, saboda mune aka turo sakon ceto.
27 For those who dwell in Jerusalem, and their rulers, because they did not know him, nor the words of the prophets, which are read every sabbath-day, have fulfilled them in condemning him.
Saboda wadanda ke zaune cikin Urushalima, da masu mulkinsu, ba su gane shi ba, kuma sun cika fadin annabawa da a ke karantawa kowace ranar Asabaci ta wurin kashe shi.
28 And though they found no cause of death, yet they demanded of Pilate that he should be slain.
Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi.
29 And when they had fulfilled all that was written of him, they took him down from the tree, and laid him in a sepulcher.
Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.
30 But God raised him from the dead.
Amma Allah ya tashe shi daga matattu.
31 And he was seen for many days by those who came up with him from Galilee to Jerusalem, who are his witnesses to the people.
Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.
32 And we preach to you good news concerning the promise made to our fathers,
Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu.
33 that God has fulfilled the same to us, their children, by raising up Jesus, as it is written in the second Psalm: Thou art my Son, this day have I begotten thee.
Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: ''Kai da na ne yau na zama mahaifinka.''
34 But that he raised him from the dead, no more to return to corruption, he has spoken thus: I will give you the sure mercies of David.
Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: ''Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu.''
35 For which reason he says also in another Psalm: Thou wilt not suffer thy Holy One to see corruption.
Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.'
36 For David, after serving the purpose of God in his own generation, fell asleep, and was laid with his fathers, and saw corruption.
Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba,
37 But he whom God raised up did not see corruption.
amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.
38 Be it known to you, therefore, brethren, that through this man is preached to you the remission of sins:
'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai.
39 and by him, every one that believes is justified from all things, from which you could not be justified by the law of Moses.
Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.
40 Take heed, therefore, lest that which is spoken in the prophets come upon you:
Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku:
41 Behold, you despisers, and wonder, and perish. For I work a work in your days, a work which you will not believe, though one fully declare it to you.
'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku.”
42 And as they were departing from the synagogue, they were requested to speak these things to them on the next sabbath.
Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa.
43 Now, after the congregation was dismissed, many of the Jews and religious proselytes followed Paul and Barnabas, who spoke to them, and persuaded them to continue faithful to the grace of God.
Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.
44 And on the next sabbath-day, almost the whole city met together to hear the word of God.
Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji.
45 But when the Jews saw the multitudes, they were filled with envy, and spoke against those things which were spoken by Paul, contradicting and reviling.
Sa'adda Yahudawa suka ga taron jama'a, sai suka cika da kishi suna karyata abubuwan da Bulus ya fada suka kuma aibata shi.
46 But Paul and Barnabas, speaking boldly, said: It was necessary that the word of God should be spoken to you first: but since you reject it, and judge yourselves unworthy of eternal life, lo! we turn to tho Gentiles. (aiōnios )
Amma Bulus da Barnaba sun yi magana gabagadi suka ce, “Dole ne a fara fada maku maganar Allah. Amma da yake kun ture ta, kun nuna baku cancanci rai madawwami ba soboda haka zamu juya ga al'ummai. (aiōnios )
47 For thus has the Lord given us commandment: I have placed thee for a light to the Gentiles, that thou mayest be for salvation to the most distant part of the earth.
Don haka Ubangiji ya umarce mu, cewa, 'Na sa ku haske ga al'ummai, saboda ku kawo ceto ga iyakar duniya.'”
48 When the Gentiles heard this they rejoiced, and glorified the word of the Lord; and as many as were determined to obtain eternal life, believed. (aiōnios )
Da al'ummai suka ji haka, sai suka yi murna suka kuma yabi kalmar Ubangiji. Dukan wadanda aka kaddarawa samin rai madawwami suka tuba. (aiōnios )
49 And the word of the Lord was published throughout the whole of that region.
Kalmar Ubangiji kuwa ta bazu a kowanne bangaren yankin.
50 But the Jews in cited the devout and influential women, and the first men of the city, and raised a persecution against Paul and Barnabas, and expelled them from their borders.
Amma Yahudawan suka zuga wadansu mata masu sujada, masu daraja da kuma shugabannin mazan garin. Wannan ya tayar da tsanani ga Bulus da Barnaba har suka fitar da su daga iyakar garinsu.
51 But they shook off the dust from their feet against them, and went to Iconium.
Amma Bulus da Barnaba suka kade masu kurar kafarsu. Suka tafi garin Ikoniya.
52 And the disciples were filled with joy and the Holy Spirit.
Amma almajiran suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.