< Psalms 25 >
1 [A Psalm] of David. Unto thee, O Jehovah, do I lift up my soul.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 O my God, in thee have I trusted, Let me not be put to shame; Let not mine enemies triumph over me.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Yea, none that wait for thee shall be put to shame: They shall be put to shame that deal treacherously without cause.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Show me thy ways, O Jehovah; Teach me thy paths.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Guide me in thy truth, and teach me; For thou art the God of my salvation; For thee do I wait all the day.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Remember, O Jehovah, thy tender mercies and thy lovingkindness; For they have been ever of old.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Remember not the sins of my youth, nor my transgressions: According to thy lovingkindness remember thou me, For thy goodness’ sake, O Jehovah.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Good and upright is Jehovah: Therefore will he instruct sinners in the way.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 The meek will he guide in justice; And the meek will he teach his way.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 All the paths of Jehovah are lovingkindness and truth Unto such as keep his covenant and his testimonies.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 For thy name’s sake, O Jehovah, Pardon mine iniquity, for it is great.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 What man is he that feareth Jehovah? Him shall he instruct in the way that he shall choose.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 His soul shall dwell at ease; And his seed shall inherit the land.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 The friendship of Jehovah is with them that fear him; And he will show them his covenant.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mine eyes are ever toward Jehovah; For he will pluck my feet out of the net.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Turn thee unto me, and have mercy upon me; For I am desolate and afflicted.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 The troubles of my heart are enlarged: Oh bring thou me out of my distresses.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Consider mine affliction and my travail; And forgive all my sins.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Consider mine enemies, for they are many; And they hate me with cruel hatred.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Oh keep my soul, and deliver me: Let me not be put to shame, for I take refuge in thee.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Let integrity and uprightness preserve me, For I wait for thee.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Redeem Israel, O God, Out of all his troubles.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!