< Psalms 104 >

1 Bless Jehovah, O my soul. O Jehovah my God, thou art very great; Thou art clothed with honor and majesty:
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2 Who coverest thyself with light as with a garment; Who stretchest out the heavens like a curtain;
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3 Who layeth the beams of his chambers in the waters; Who maketh the clouds his chariot; Who walketh upon the wings of the wind;
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4 Who maketh winds his messengers; Flames of fire his ministers;
Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5 Who laid the foundations of the earth, That it should not be moved for ever.
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6 Thou coveredst it with the deep as with a vesture; The waters stood above the mountains.
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7 At thy rebuke they fled; At the voice of thy thunder they hasted away
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8 (The mountains rose, the valleys sank down) Unto the place which thou hadst founded for them.
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9 Thou hast set a bound that they may not pass over; That they turn not again to cover the earth.
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
10 He sendeth forth springs into the valleys; They run among the mountains;
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11 They give drink to every beast of the field; The wild asses quench their thirst.
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12 By them the birds of the heavens have their habitation; They sing among the branches.
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13 He watereth the mountains from his chambers: The earth is filled with the fruit of thy works.
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14 He causeth the grass to grow for the cattle, And herb for the service of man; That he may bring forth food out of the earth,
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15 And wine that maketh glad the heart of man, [And] oil to make his face to shine, And bread that strengtheneth man’s heart.
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16 The trees of Jehovah are filled [with moisture], The cedars of Lebanon, which he hath planted;
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17 Where the birds make their nests: As for the stork, the fir-trees are her house.
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18 The high mountains are for the wild goats; The rocks are a refuge for the conies.
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19 He appointed the moon for seasons: The sun knoweth his going down.
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20 Thou makest darkness, and it is night, Wherein all the beasts of the forest creep forth.
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21 The young lions roar after their prey, And seek their food from God.
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22 The sun ariseth, they get them away, And lay them down in their dens.
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23 Man goeth forth unto his work And to his labor until the evening.
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
24 O Jehovah, how manifold are thy works! In wisdom hast thou made them all: The earth is full of thy riches.
Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
25 Yonder is the sea, great and wide, Wherein are things creeping innumerable, Both small and great beasts.
Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
26 There go the ships; There is leviathan, whom thou hast formed to play therein.
A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
27 These wait all for thee, That thou mayest give them their food in due season.
Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
28 Thou givest unto them, they gather; Thou openest thy hand, they are satisfied with good.
Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
29 Thou hidest thy face, they are troubled; Thou takest away their breath, they die, And return to their dust.
Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
30 Thou sendest forth thy Spirit, they are created; And thou renewest the face of the ground.
Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
31 Let the glory of Jehovah endure for ever; Let Jehovah rejoice in his works:
Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
32 Who looketh on the earth, and it trembleth; He toucheth the mountains, and they smoke.
shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
33 I will sing unto Jehovah as long as I live: I will sing praise to my God while I have any being.
Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
34 Let my meditation be sweet unto him: I will rejoice in Jehovah.
Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
35 Let sinners be consumed out of the earth. And let the wicked be no more. Bless Jehovah, O my soul. Praise ye Jehovah.
Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.

< Psalms 104 >