< Psalms 103 >

1 [A Psalm] of David. Bless Jehovah, O my soul; And all that is within me, [bless] his holy name.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Bless Jehovah, O my soul, And forget not all his benefits:
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 Who forgiveth all thine iniquities; Who healeth all thy diseases;
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 Who redeemeth thy life from destruction; Who crowneth thee with lovingkindness and tender mercies;
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 Who satisfieth thy desire with good things, [So that] thy youth is renewed like the eagle.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 Jehovah executeth righteous acts, And judgments for all that are oppressed.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 He made known his ways unto Moses, His doings unto the children of Israel.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 Jehovah is merciful and gracious, Slow to anger, and abundant in lovingkindness.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 He will not always chide; Neither will he keep [his anger] for ever.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 He hath not dealt with us after our sins, Nor rewarded us after our iniquities.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 For as the heavens are high above the earth, So great is his lovingkindness toward them that fear him.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 As far as the east is from the west, So far hath he removed our transgressions from us.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 Like as a father pitieth his children, So Jehovah pitieth them that fear him.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 For he knoweth our frame; He remembereth that we are dust.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 As for man, his days are as grass; As a flower of the field, so he flourisheth.
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 For the wind passeth over it, and it is gone; And the place thereof shall know it no more.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 But the lovingkindness of Jehovah is from everlasting to everlasting upon them that fear him, And his righteousness unto children’s children;
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 To such as keep his covenant, And to those that remember his precepts to do them.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 Jehovah hath established his throne in the heavens; And his kingdom ruleth over all.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Bless Jehovah, ye his angels, That are mighty in strength, that fulfil his word, Hearkening unto the voice of his word.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Bless Jehovah, all ye his hosts, Ye ministers of his, that do his pleasure.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Bless Jehovah, all ye his works, In all places of his dominion: Bless Jehovah, O my soul.
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Psalms 103 >