< Proverbs 8 >

1 Doth not wisdom cry, And understanding put forth her voice?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 On the top of high places by the way, Where the paths meet, she standeth;
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Beside the gates, at the entry of the city, At the coming in at the doors, she crieth aloud:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 Unto you, O men, I call; And my voice is to the sons of men.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 O ye simple, understand prudence; And, ye fools, be of an understanding heart.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Hear, for I will speak excellent things; And the opening of my lips shall be right things.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 For my mouth shall utter truth; And wickedness is an abomination to my lips.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 All the words of my mouth are in righteousness; There is nothing crooked or perverse in them.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 They are all plain to him that understandeth, And right to them that find knowledge.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Receive my instruction, and not silver; And knowledge rather than choice gold.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 For wisdom is better than rubies; And all the things that may be desired are not to be compared unto it.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 I wisdom have made prudence my dwelling, And find out knowledge [and] discretion.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 The fear of Jehovah is to hate evil: Pride, and arrogancy, and the evil way, And the perverse mouth, do I hate.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Counsel is mine, and sound knowledge: I am understanding; I have might.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 By me kings reign, And princes decree justice.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 By me princes rule, And nobles, [even] all the judges of the earth.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 I love them that love me; And those that seek me diligently shall find me.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Riches and honor are with me; [Yea], durable wealth and righteousness.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 My fruit is better than gold, yea, than fine gold; And my revenue than choice silver.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 I walk in the way of righteousness, In the midst of the paths of justice;
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 That I may cause those that love me to inherit substance, And that I may fill their treasuries.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Jehovah possessed me in the beginning of his way, Before his works of old.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 I was set up from everlasting, from the beginning, Before the earth was.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 When there were no depths, I was brought forth, When there were no fountains abounding with water.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Before the mountains were settled, Before the hills was I brought forth;
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 While as yet he had not made the earth, nor the fields, Nor the beginning of the dust of the world.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 When he established the heavens, I was there: When he set a circle upon the face of the deep,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 When he made firm the skies above, When the fountains of the deep became strong,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 When he gave to the sea its bound, That the waters should not transgress his commandment, When he marked out the foundations of the earth;
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Then I was by him, [as] a master workman; And I was daily [his] delight, Rejoicing always before him,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Rejoicing in his habitable earth; And my delight was with the sons of men.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Now therefore, [my] sons, hearken unto me; For blessed are they that keep my ways.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Hear instruction, and be wise, And refuse it not.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Blessed is the man that heareth me, Watching daily at my gates, Waiting at the posts of my doors.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 For whoso findeth me findeth life, And shall obtain favor of Jehovah.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 But he that sinneth against me wrongeth his own soul: All they that hate me love death.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbs 8 >