< Joshua 18 >

1 And the whole congregation of the children of Israel assembled themselves together at Shiloh, and set up the tent of meeting there: and the land was subdued before them.
Isra’ilawa duka suka taru a Shilo suka kafa tenti inda za su dinga taruwa. Yanzu ƙasar tana ƙarƙashin mulkinsu,
2 And there remained among the children of Israel seven tribes, which had not yet divided their inheritance.
amma akwai sauran kabilu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su samu rabon gādonsu ba tukuna.
3 And Joshua said unto the children of Israel, How long are ye slack to go in to possess the land, which Jehovah, the God of your fathers, hath given you?
Saboda haka Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na iyayenku ya ba ku?
4 Appoint for you three men of each tribe: and I will send them, and they shall arise, and walk through the land, and describe it according to their inheritance; and they shall come unto me.
Ku ba da mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su zagaya dukan ƙasar su rubuta bayani game da ita, bisa ga yadda za a raba ta gādo ga kowace kabila, sa’an nan su dawo wurina.
5 And they shall divide it into seven portions: Judah shall abide in his border on the south, and the house of Joseph shall abide in their border on the north.
Za ku raba ƙasar kashi bakwai. Mutanen Yahuda za su ci gaba da kasancewa a wurin da suke a kudu, sai kuma mutanen Yusuf a wurin da suke a arewa.
6 And ye shall describe the land into seven portions, and bring [the description] hither to me; and I will cast lots for you here before Jehovah our God.
Bayan kun auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sai ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuma in yi muku ƙuri’a a gaban Ubangiji Allahnmu.
7 For the Levites have no portion among you; for the priesthood of Jehovah is their inheritance: and Gad and Reuben and the half-tribe of Manasseh have received their inheritance beyond the Jordan eastward, which Moses the servant of Jehovah gave them.
Lawiyawa ba su da rabo a cikinku, domin aikin firistocin da suke yi wa Ubangiji shi ne gādonsu. Gad, Ruben da rabin kabilar Manasse kuwa sun riga sun samu gādonsu a gabashin gefen Urdun, Musa bawan Ubangiji ya ba su.”
8 And the men arose, and went: and Joshua charged them that went to describe the land, saying, Go and walk through the land, and describe it, and come again to me; and I will cast lots for you here before Jehovah in Shiloh.
Da mutanen za su kama hanya su je su zāna yadda ƙasar take, Yoshuwa ya umarce su cewa, “Ku je ku ga yadda ƙasar take. Sa’an nan ku dawo wurina, zan yi muku ƙuri’a a nan Shilo a gaban Ubangiji.”
9 And the men went and passed through the land, and described it by cities into seven portions in a book; and they came to Joshua unto the camp at Shiloh.
Mutanen kuwa suka tafi suka bi ta cikin ƙasar, suka bayyana yadda take a rubuce, gari-gari, kashi bakwai, suka koma wurin Yoshuwa a Shilo.
10 And Joshua cast lots for them in Shiloh before Jehovah: and there Joshua divided the land unto the children of Israel according to their divisions.
Sai Yoshuwa ya yi musu ƙuri’a a gaban Ubangiji, a nan ne ya raba wa Isra’ilawa ƙasar bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
11 And the lot of the tribe of the children of Benjamin came up according to their families: and the border of their lot went out between the children of Judah and the children of Joseph.
Ƙuri’ar kabilar Benyamin bisa ga iyalansu. Rabonsu ya kama daga ƙasar da take tsakanin kabilar Yahuda da ta Yusuf.
12 And their border on the north quarter was from the Jordan; and the border went up to the side of Jericho on the north, and went up through the hill-country westward; and the goings out thereof were at the wilderness of Beth-aven.
Daga gefen arewa, iyakarsu ta kama ne daga Urdun, ta wuce arewa a gangaren Yeriko, ta nufi yamma cikin ƙasar kan tudu, ta fito a jejin Bet-Awen.
13 And the border passed along from thence to Luz, to the side of Luz (the same is Beth-el), southward; and the border went down to Ataroth-addar, by the mountain that lieth on the south of Beth-horon the nether.
Daga can ta ƙetare zuwa gangaren Luz a kudu (wato, Betel), ta wuce zuwa Atarot Adda a tudun arewa na kwarin Bet-Horon.
14 And the border extended [thence], and turned about on the west quarter southward, from the mountain that lieth before Beth-horon southward; and the goings out thereof were at Kiriath-baal (the same is Kiriath-jearim), a city of the children of Judah: this was the west quarter.
Daga tudun da yake fuskantar Bet-Horon a kudu, iyakar ta juya kudu ta gefen yamma ta ɓullo a Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim), birnin Yahuda. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
15 And the south quarter was from the uttermost part of Kiriath-jearim; and the border went out westward, and went out to the fountain of the waters of Nephtoah;
A gefen kudu kuwa, iyakar ta fara daga ƙauyukan Kiriyat Yeyarim wajen yamma sai ta miƙe zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa.
16 and the border went down to the uttermost part of the mountain that lieth before the valley of the son of Hinnom, which is in the vale of Rephaim northward; and it went down to the valley of Hinnom, to the side of the Jebusite southward, and went down to En-rogel;
Iyakar ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskantar Kwarin Ben Hinnom, wanda yake arewa da Kwarin Refayim. Ta ci gaba ta gangara ta Kwarin Hinnom ta yi kudu kusa da birnin Yebusiyawa har zuwa En Rogel.
17 and it extended northward, and went out at En-shemesh, and went out to Geliloth, which is over against the ascent of Adummim; and it went down to the stone of Bohan the son of Reuben;
Sai ta nausa ta yi wajen arewa, zuwa En Shemesh, ta ci gaba zuwa Gelilot, wanda yake fuskantar hawan Adummim. Daga can ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ruben.
18 and it passed along to the side over against the Arabah northward, and went down unto the Arabah;
Sai ta wuce ta yi arewancin gangaren Bet-Araba, ta wuce har zuwa cikin Araba.
19 and the border passed along to the side of Beth-hoglah northward; and the goings out of the border were at the north bay of the Salt Sea, at the south end of the Jordan: this was the south border.
Sa’an nan ta wuce zuwa arewancin gangaren Bet-Hogla ta kuma ɓulla a arewancin gaɓar Tekun Gishiri, a bakin Urdun a kudu. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 And the Jordan was the border of it on the east quarter. This was the inheritance of the children of Benjamin, by the borders thereof round about, according to their families.
Urdun shi ne iyaka a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Benyamin suka gāda.
21 Now the cities of the tribe of the children of Benjamin according to their families were Jericho, and Beth-hoglah, and Emek-keziz,
Waɗannan su ne garuruwan da kabilar Benyamin suke da su na gādo. Yeriko, Bet-Hogla, Emek Keziz,
22 and Beth-arabah, and Zemaraim, and Beth-el,
Bet-Araba, Zemarayim, Betel,
23 and Avvim, and Parah, and Ophrah,
Awwim, Fara, Ofra,
24 and Chephar-ammoni, and Ophni, and Geba; twelve cities with their villages:
Kefar Ammoni, Ofni da Geba, garuruwa goma sha biyu ke nan da ƙauyukansu.
25 Gibeon, and Ramah, and Beeroth,
Akwai kuma Gibeyon, Rama, Beyerot,
26 and Mizpeh, and Chephirah, and Mozah,
Mizfa Kefira, Moza,
27 and Rekem, and Irpeel, and Taralah,
Rekem, Irfeyel, Tarala,
28 and Zelah, Eleph, and the Jebusite (the same is Jerusalem), Gibeath, [and] Kiriath; fourteen cities with their villages. This is the inheritance of the children of Benjamin according to their families.
Zela, Hayelef, birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima), Gibeya da Kiriyat, garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon kabilar Benyamin bisa ga iyalansu.

< Joshua 18 >