< Isaiah 15 >

1 The burden of Moab. For in a night Ar of Moab is laid waste, [and] brought to nought; for in a night Kir of Moab is laid waste, [and] brought to nought.
Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
2 They are gone up to Bayith, and to Dibon, to the high places, to weep: Moab waileth over Nebo, and over Medeba; on all their heads is baldness, every beard is cut off.
Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
3 In their streets they gird themselves with sackcloth; on their housetops, and in their broad places, every one waileth, weeping abundantly.
A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
4 And Heshbon crieth out, and Elealeh; their voice is heard even unto Jahaz: therefore the armed men of Moab cry aloud; his soul trembleth within him.
Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
5 My heart crieth out for Moab; her nobles [flee] unto Zoar, to Eglath-shelishi-yah: for by the ascent of Luhith with weeping they go up; for in the way of Horonaim they raise up a cry of destruction.
Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
6 For the waters of Nimrim shall be desolate; for the grass is withered away, the tender grass faileth, there is no green thing.
Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
7 Therefore the abundance they have gotten, and that which they have laid up, shall they carry away over the brook of the willows.
Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
8 For the cry is gone round about the borders of Moab; the wailing thereof unto Eglaim, and the wailing thereof unto Beer-elim.
Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
9 For the waters of Dimon are full of blood; for I will bring yet more upon Dimon, a lion upon them of Moab that escape, and upon the remnant of the land.
Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.

< Isaiah 15 >