< Genesis 49 >

1 And Jacob called unto his sons, and said: Gather yourselves together, that I may tell you that which shall befall you in the latter days.
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 Assemble yourselves, and hear, ye sons of Jacob; And hearken unto Israel your father.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 Reuben, thou art my first-born, my might, and the beginning of my strength; The pre-eminence of dignity, and the pre-eminence of power.
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 Boiling over as water, thou shalt not have the pre-eminence; Because thou wentest up to thy father’s bed; Then defiledst thou it: he went up to my couch.
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 Simeon and Levi are brethren; Weapons of violence are their swords.
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 O my soul, come not thou into their council; Unto their assembly, my glory, be not thou united; For in their anger they slew a man, And in their self-will they hocked an ox.
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 Cursed be their anger, for it was fierce; And their wrath, for it was cruel: I will divide them in Jacob, And scatter them in Israel.
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Judah, thee shall thy brethren praise: Thy hand shall be on the neck of thine enemies; Thy father’s sons shall bow down before thee.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 Judah is a lion’s whelp; From the prey, my son, thou art gone up: He stooped down, he couched as a lion, And as a lioness; who shall rouse him up?
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 The sceptre shall not depart from Judah, Nor the ruler’s staff from between his feet, Until Shiloh come; And unto him shall the obedience of the peoples be.
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 Binding his foal unto the vine, And his ass’s colt unto the choice vine; He hath washed his garments in wine, And his vesture in the blood of grapes:
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 His eyes shall be red with wine, And his teeth white with milk.
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 Zebulun shall dwell at the haven of the sea; And he shall be for a haven of ships; And his border shall be upon Sidon.
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 Issachar is a strong ass, Couching down between the sheepfolds:
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 And he saw a resting-place that it was good, And the land that it was pleasant; And he bowed his shoulder to bear, And became a servant under taskwork.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 Dan shall judge his people, As one of the tribes of Israel.
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Dan shall be a serpent in the way, An adder in the path, That biteth the horse’s heels, So that his rider falleth backward.
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 I have waited for thy salvation, O Jehovah.
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 Gad, a troop shall press upon him; But he shall press upon their heel.
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 Out of Asher his bread shall be fat, And he shall yield royal dainties.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 Naphtali is a hind let loose: He giveth goodly words.
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 Joseph is a fruitful bough, A fruitful bough by a fountain; His branches run over the wall.
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 The archers have sorely grieved him, And shot at him, and persecuted him:
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 But his bow abode in strength, And the arms of his hands were made strong, By the hands of the Mighty One of Jacob (From thence is the shepherd, the stone of Israel),
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 Even by the God of thy father, who shall help thee, And by the Almighty, who shall bless thee, With blessings of heaven above, Blessings of the deep that coucheth beneath, Blessings of the breasts, and of the womb.
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 The blessings of thy father Have prevailed above the blessings of my progenitors Unto the utmost bound of the everlasting hills: They shall be on the head of Joseph, And on the crown of the head of him that was separate from his brethren.
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 Benjamin is a wolf that raveneth: In the morning he shall devour the prey, And at even he shall divide the spoil.
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 All these are the twelve tribes of Israel: and this is it that their father spake unto them and blessed them; every one according to his blessing he blessed them.
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 And he charged them, and said unto them, I am to be gathered unto my people: bury me with my fathers in the cave that is in the field of Ephron the Hittite,
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 in the cave that is in the field of Machpelah, which is before Mamre, in the land of Canaan, which Abraham bought with the field from Ephron the Hittite for a possession of a burying-place.
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 There they buried Abraham and Sarah his wife; there they buried Isaac and Rebekah his wife; and there I buried Leah—
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
32 the field and the cave that is therein, which was purchased from the children of Heth.
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 And when Jacob made an end of charging his sons, he gathered up his feet into the bed, and yielded up the ghost, and was gathered unto his people.
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.

< Genesis 49 >