< Exodus 31 >

1 And Jehovah spake unto Moses, saying,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 See, I have called by name Bezalel the son of Uri, the son of Hur, of the tribe of Judah:
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 and I have filled him with the Spirit of God, in wisdom, and in understanding, and in knowledge, and in all manner of workmanship,
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4 to devise skilful works, to work in gold, and in silver, and in brass,
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5 and in cutting of stones for setting, and in carving of wood, to work in all manner of workmanship.
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6 And I, behold, I have appointed with him Oholiab, the son of Ahisamach, of the tribe of Dan; and in the heart of all that are wise-hearted I have put wisdom, that they may make all that I have commanded thee:
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
7 the tent of meeting, and the ark of the testimony, and the mercy-seat that is thereupon, and all the furniture of the Tent,
Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
8 and the table and its vessels, and the pure candlestick with all its vessels, and the altar of incense,
tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
9 and the altar of burnt-offering with all its vessels, and the laver and its base,
bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
10 and the finely wrought garments, and the holy garments for Aaron the priest, and the garments of his sons, to minister in the priest’s office,
da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
11 and the anointing oil, and the incense of sweet spices for the holy place: according to all that I have commanded thee shall they do.
da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
12 And Jehovah spake unto Moses, saying,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
13 Speak thou also unto the children of Israel, saying, Verily ye shall keep my sabbaths: for it is a sign between me and you throughout your generations; that ye may know that I am Jehovah who sanctifieth you.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
14 Ye shall keep the sabbath therefore; for it is holy unto you: every one that profaneth it shall surely be put to death; for whosoever doeth any work therein, that soul shall be cut off from among his people.
“‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
15 Six days shall work be done, but on the seventh day is a sabbath of solemn rest, holy to Jehovah: whosoever doeth any work on the sabbath day, he shall surely be put to death.
Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
16 Wherefore the children of Israel shall keep the sabbath, to observe the sabbath throughout their generations, for a perpetual covenant.
Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
17 It is a sign between me and the children of Israel for ever: for in six days Jehovah made heaven and earth, and on the seventh day he rested, and was refreshed.
Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
18 And he gave unto Moses, when he had made an end of communing with him upon mount Sinai, the two tables of the testimony, tables of stone, written with the finger of God.
Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.

< Exodus 31 >