< Deuteronomy 9 >
1 Hear, O Israel: thou art to pass over the Jordan this day, to go in to dispossess nations greater and mightier than thyself, cities great and fortified up to heaven,
Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
2 a people great and tall, the sons of the Anakim, whom thou knowest, and of whom thou hast heard say, Who can stand before the sons of Anak?
Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
3 Know therefore this day, that Jehovah thy God is he who goeth over before thee as a devouring fire; he will destroy them, and he will bring them down before thee: so shalt thou drive them out, and make them to perish quickly, as Jehovah hath spoken unto thee.
Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
4 Speak not thou in thy heart, after that Jehovah thy God hath thrust them out from before thee, saying, For my righteousness Jehovah hath brought me in to possess this land; whereas for the wickedness of these nations Jehovah doth drive them out from before thee.
Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
5 Not for thy righteousness, or for the uprightness of thy heart, dost thou go in to possess their land; but for the wickedness of these nations Jehovah thy God doth drive them out from before thee, and that he may establish the word which Jehovah sware unto thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob.
Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
6 Know therefore, that Jehovah thy God giveth thee not this good land to possess it for thy righteousness; for thou art a stiffnecked people.
Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
7 Remember, forget thou not, how thou provokedst Jehovah thy God to wrath in the wilderness: from the day that thou wentest forth out of the land of Egypt, until ye came unto this place, ye have been rebellious against Jehovah.
Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
8 Also in Horeb ye provoked Jehovah to wrath, and Jehovah was angry with you to destroy you.
A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
9 When I was gone up into the mount to receive the tables of stone, even the tables of the covenant which Jehovah made with you, then I abode in the mount forty days and forty nights; I did neither eat bread nor drink water.
Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
10 And Jehovah delivered unto me the two tables of stone written with the finger of God; and on them [was written] according to all the words, which Jehovah spake with you in the mount out of the midst of the fire in the day of the assembly.
Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
11 And it came to pass at the end of forty days and forty nights, that Jehovah gave me the two tables of stone, even the tables of the covenant.
A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
12 And Jehovah said unto me, Arise, get thee down quickly from hence; for thy people that thou hast brought forth out of Egypt have corrupted themselves; they are quickly turned aside out of the way which I commanded them; they have made them a molten image.
Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
13 Furthermore Jehovah spake unto me, saying, I have seen this people, and, behold, it is a stiffnecked people:
Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
14 let me alone, that I may destroy them, and blot out their name from under heaven; and I will make of thee a nation mightier and greater than they.
Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
15 So I turned and came down from the mount, and the mount was burning with fire: and the two tables of the covenant were in my two hands.
Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
16 And I looked, and, behold, ye had sinned against Jehovah your God; ye had made you a molten calf: ye had turned aside quickly out of the way which Jehovah had commanded you.
Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
17 And I took hold of the two tables, and cast them out of my two hands, and brake them before your eyes.
Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
18 And I fell down before Jehovah, as at the first, forty days and forty nights; I did neither eat bread nor drink water; because of all your sin which ye sinned, in doing that which was evil in the sight of Jehovah, to provoke him to anger.
Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
19 For I was afraid of the anger and hot displeasure, wherewith Jehovah was wroth against you to destroy you. But Jehovah hearkened unto me that time also.
Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
20 And Jehovah was very angry with Aaron to destroy him: and I prayed for Aaron also at the same time.
Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
21 And I took your sin, the calf which ye had made, and burnt it with fire, and stamped it, grinding it very small, until it was as fine as dust: and I cast the dust thereof into the brook that descended out of the mount.
Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
22 And at Taberah, and at Massah, and at Kibroth-hattaavah, ye provoked Jehovah to wrath.
Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
23 And when Jehovah sent you from Kadesh-barnea, saying, Go up and possess the land which I have given you; then ye rebelled against the commandment of Jehovah your God, and ye believed him not, nor hearkened to his voice.
Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
24 Ye have been rebellious against Jehovah from the day that I knew you.
Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
25 So I fell down before Jehovah the forty days and forty nights that I fell down, because Jehovah had said he would destroy you.
Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
26 And I prayed unto Jehovah, and said, O Lord Jehovah, destroy not thy people and thine inheritance, that thou hast redeemed through thy greatness, that thou hast brought forth out of Egypt with a mighty hand.
Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
27 Remember thy servants, Abraham, Isaac, and Jacob; look not unto the stubbornness of this people, nor to their wickedness, nor to their sin,
Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
28 lest the land whence thou broughtest us out say, Because Jehovah was not able to bring them into the land which he promised unto them, and because he hated them, he hath brought them out to slay them in the wilderness.
In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
29 Yet they are thy people and thine inheritance, which thou broughtest out by thy great power and by thine outstretched arm.
Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”