< Acts 2 >

1 And when the day of Pentecost was now come, they were all together in one place.
Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
2 And suddenly there came from heaven a sound as of the rushing of a mighty wind, and it filled all the house where they were sitting.
Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
3 And there appeared unto them tongues parting asunder, like as of fire; and it sat upon each one of them.
Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
4 And they were all filled with the Holy Spirit, and began to speak with other tongues, as the Spirit gave them utterance.
Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
5 Now there were dwelling at Jerusalem Jews, devout men, from every nation under heaven.
A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
6 And when this sound was heard, the multitude came together, and were confounded, because that every man heard them speaking in his own language.
Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
7 And they were all amazed and marvelled, saying, Behold, are not all these that speak Galilæans?
Suka yi mamaki matuka; suka ce, ''Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
8 And how hear we, every man in our own language wherein we were born?
Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
9 Parthians and Medes and Elamites, and the dwellers in Mesopotamia, in Judæa and Cappadocia, in Pontus and Asia,
Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
10 in Phrygia and Pamphylia, in Egypt and the parts of Libya about Cyrene, and sojourners from Rome, both Jews and proselytes,
cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
11 Cretans and Arabians, we hear them speaking in our tongues the mighty works of God.
Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.''
12 And they were all amazed, and were perplexed, saying one to another, What meaneth this?
Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, ''Menene ma'anar wannan?''
13 But others mocking said, They are filled with new wine.
Amma wasu suka yi ba'a suka ce, ''Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.''
14 But Peter, standing up with the eleven, lifted up his voice, and spake forth unto them, [saying], Ye men of Judæa, and all ye that dwell at Jerusalem, be this known unto you, and give ear unto my words.
Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, ''Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
15 For these are not drunken, as ye suppose; seeing it is [but] the third hour of the day;
Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
16 but this is that which hath been spoken through the prophet Joel:
Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
17 And it shall be in the last days, saith God, I will pour forth of my Spirit upon all flesh: And your sons and your daughters shall prophesy, And your young men shall see visions, And your old men shall dream dreams:
Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
18 Yea and on my servants and on my handmaidens in those days Will I pour forth of my Spirit; and they shall prophesy.
Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
19 And I will show wonders in the heaven above, And signs on the earth beneath; Blood, and fire, and vapor of smoke:
Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
20 The sun shall be turned into darkness, And the moon into blood, Before the day of the Lord come, That great and notable [day]:
Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
21 And it shall be, that whosoever shall call on the name of the Lord shall be saved.
Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
22 Ye men of Israel, hear these words: Jesus of Nazareth, a man approved of God unto you by mighty works and wonders and signs which God did by him in the midst of you, even as ye yourselves know;
Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani.
23 him, being delivered up by the determinate counsel and foreknowledge of God, ye by the hand of lawless men did crucify and slay:
Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi.
24 whom God raised up, having loosed the pangs of death: because it was not possible that he should be holden of it.
Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
25 For David saith concerning him, I beheld the Lord always before my face; For he is on my right hand, that I should not be moved:
Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita.
26 Therefore my heart was glad, and my tongue rejoiced; Moreover my flesh also shall dwell in hope:
Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
27 Because thou wilt not leave my soul unto Hades, Neither wilt thou give thy Holy One to see corruption. (Hadēs g86)
Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. (Hadēs g86)
28 Thou madest known unto me the ways of life; Thou shalt make me full of gladness with thy countenance.
Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
29 Brethren, I may say unto you freely of the patriarch David, that he both died and was buried, and his tomb is with us unto this day.
'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau.
30 Being therefore a prophet, and knowing that God had sworn with an oath to him, that of the fruit of his loins he would set [one] upon his throne;
Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa.
31 he foreseeing [this] spake of the resurrection of the Christ, that neither was he left unto Hades, nor did his flesh see corruption. (Hadēs g86)
Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.' (Hadēs g86)
32 This Jesus did God raise up, whereof we all are witnesses.
Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne.
33 Being therefore by the right hand of God exalted, and having received of the Father the promise of the Holy Spirit, he hath poured forth this, which ye see and hear.
Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
34 For David ascended not into the heavens: but he saith himself, The Lord said unto my Lord, Sit thou on my right hand,
Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, ''Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
35 Till I make thine enemies the footstool of thy feet.
har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'''
36 Let all the house of Israel therefore know assuredly, that God hath made him both Lord and Christ, this Jesus whom ye crucified.
Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
37 Now when they heard [this], they were pricked in their heart, and said unto Peter and the rest of the apostles, Brethren, what shall we do?
Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '''Yan'uwa me za mu yi?''
38 And Peter [said] unto them, Repent ye, and be baptized every one of you in the name of Jesus Christ unto the remission of your sins; and ye shall receive the gift of the Holy Spirit.
Sai Bitrus ya ce masu, ''Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
39 For to you is the promise, and to your children, and to all that are afar off, [even] as many as the Lord our God shall call unto him.
Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.''
40 And with many other words he testified, and exhorted them, saying, Save yourselves from this crooked generation.
Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, ''Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.''
41 They then that received his word were baptized: and there were added [unto them] in that day about three thousand souls.
Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku.
42 And they continued stedfastly in the apostles’ teaching and fellowship, in the breaking of bread and the prayers.
Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
43 And fear came upon every soul: and many wonders and signs were done through the apostles.
Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin.
44 And all that believed were together, and had all things common;
Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne,
45 and they sold their possessions and goods, and parted them to all, according as any man had need.
kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
46 And day by day, continuing stedfastly with one accord in the temple, and breaking bread at home, they took their food with gladness and singleness of heart,
A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya;
47 praising God, and having favor with all the people. And the Lord added to them day by day those that were saved.
Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.

< Acts 2 >