< Romans 8 >

1 Consequently nothing is condemnation now to those in Christ Jesus, who walk not according to flesh but according to Spirit.
Saboda haka, yanzu babu hukunci don waɗanda suke cikin Kiristi Yesu,
2 For the law of the Spirit of life in Christ Jesus freed me from the law of sin and of death.
gama ta wurin Kiristi Yesu dokar Ruhu mai ba da rai ta’yantar da ni daga Dokar Musa.
3 For the impotence of the law, in that it was weak because of the flesh, God, having sent his own Son in a form of flesh of sin, and concerning sin, condemned sin in the flesh,
Gama abin da dokar ba tă iya yi saboda kāsawar mutuntaka ba, Allah ya yi shi sa’ad da ya aiko da Ɗansa a kamannin mutum mai zunubi, don yă zama hadaya ta zunubi. Ta haka, ya hukunta zunubi a cikin mutum mai zunubi.
4 so that the justice of the law might be fulfilled in us, those who walk not according to flesh, but according to Spirit.
Ya yi haka domin yă cika bukatun adalcin doka a cikinmu, mu da ba ma rayuwa bisa ga mutuntaka, sai dai bisa ga Ruhu.
5 For those who are according to flesh think about the things of the flesh, but those according to Spirit the things of the Spirit.
Waɗanda suke rayuwa bisa ga mutuntaka sun kafa hankulansu a kan sha’awace-shawa’acen jiki; amma waɗanda suke rayuwa bisa ga Ruhu sun kafa hankulansu a kan abubuwan da Ruhu yake so.
6 For the mentality of the flesh is death, but the mentality of the Spirit is life and peace.
Ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga al’amuran Ruhu kuwa rai ne da salama;
7 Because the mentality of the flesh is enmity against God, for it is not submissive to the law of God, for neither is it able.
hankalin mai zunubi na gāba da Allah. Ba ya biyayya da dokar Allah, ba kuwa zai iya yin haka ba.
8 And those who are in flesh cannot please God.
Waɗanda mutuntaka yake mulkinsu ba za su iya su gamshi Allah ba.
9 But ye are not in flesh but in Spirit, if indeed the Spirit of God dwells in you. But if any man does not have the Spirit of Christ, this man is not of him.
Ku kam, ana mulkinku ba ta wurin mutuntaka ba, sai dai ta wurin Ruhu, in Ruhun Allah yana zaune a cikinku. In kuma wani ba shi da Ruhun Kiristi, shi ba na Kiristi ba ne.
10 And if Christ is in you, the body is indeed dead because of sin, but the spirit is life because of righteousness.
Amma in Kiristi yana a cikinku, jikinku matacce ne saboda zunubi, duk da haka ruhunku yana a raye saboda adalci.
11 But if the Spirit of him who raised up Jesus from the dead dwells in you, he who raised up the Christ from the dead will also give life to your mortal bodies through his Spirit that dwells in you.
In kuwa Ruhu wannan da ya tā da Yesu daga matattu yana zama a cikinku, shi wanda ya tā da Kiristi daga matattu zai ba da rai ga jikunanku masu mutuwa ta wurin Ruhunsa, wanda yake zama a cikinku.
12 So then, brothers, we are debtors, not to the flesh to live according to flesh.
Saboda haka’yan’uwa, muna da hakki, amma ba na wanda za mu yi rayuwar mutuntaka da yake so ba.
13 For if ye live according to flesh, ye are going to die, but if in spirit ye kill the deeds of the body, ye will live.
Gama in kuna rayuwa bisa ga mutuntaka, za ku mutu; amma in ta wurin Ruhu kuka kashe ayyukan jikin nan, za ku rayu.
14 For as many as are led by the Spirit of God, these are sons of God.
Domin waɗanda Ruhun Allah yake bi da su ne’ya’yan Allah.
15 For ye did not receive a spirit of bondage again for fear, but ye received a spirit of adoption, whereby we cry, Abba, Father.
Gama ba ku karɓi ruhun da ya mai da ku bayi da za ku sāke jin tsoro ba ne, sai dai kun karɓi Ruhun zaman ɗa. Ta wurinsa kuwa muke kira, “Abba, Uba.”
16 The Spirit itself testifies with our spirit, that we are children of God.
Ruhu kansa yana ba da shaida tare da ruhunmu cewa mu’ya’yan Allah ne.
17 And if children, also heirs, heirs indeed of God, and joint-heirs with Christ; if indeed we suffer jointly, so that we may also be glorified jointly.
In kuwa mu’ya’ya ne, to, mu magāda ne, magādan Allah da kuma abokan gādo tare da Kiristi, in kuwa muna tarayya a cikin shan wuyarsa to, za mu yi tarayya a cikin ɗaukakarsa.
18 For I reckon that the sufferings of the present time are not comparable to the glory that is going to be revealed for us.
A ganina, wuyar da muke sha a wannan lokaci ba su isa a kwatanta da ɗaukakar da za a bayyana a cikinmu ba.
19 For the eager expectation of the creation is waiting for the manifestation of the sons of God.
Halitta tana jira da marmari ta ƙosa ta ga bayyanuwar’ya’yan Allah.
20 For the creation was made subject to futility, not willingly, but because of him who subjected it in hope.
Gama an sa halitta a cikin wulaƙanci, ba da son ta ba, sai dai ta wurin nufin wannan da ya mai da ita haka, da bege
21 Because the creation itself will also be freed from the bondage of corruption into the liberty of the glory of the children of God.
cewa za a’yantar da halitta kanta daga bautarta ga ruɓewa a kuma kawo ta cikin’yancin ɗaukakar’ya’yan Allah.
22 For we know that the whole creation is groaning and travailing together until now.
Mun san cewa dukan halitta tana nishi sai ka ce mace mai naƙuda har yă zuwa wannan lokaci.
23 And not only so, but also ourselves who have the first fruit of the Spirit. And we ourselves groan within ourselves, waiting for adoption, the redemption of our body.
Ba haka kaɗai ba ma, mu kanmu da muke da nunan fari na Ruhu, muna nishi a ciki-cikinmu yayinda muke jira da marmari a maishe mu’ya’yan riƙo na Allah, fansar jikunanmu.
24 For we were saved to hope. But hope that is seen is not hope. For what is seen, why also hope for that?
Gama a wannan begen ne muka sami ceto. Amma begen da ake gani ba bege ba ne sam. Wa yake begen abin da ya riga ya samu?
25 But if we hope for what we do not see, we wait through patience.
Amma in muna begen abin da ba mu riga mun samu tukuna ba, mukan jira da haƙuri.
26 And likewise also the Spirit helps our weaknesses, for we know not what we would pray for as we ought, but the Spirit itself intercedes for us with inexpressible groanings.
Haka nan ma, Ruhu yana taimakonmu cikin rashin ƙarfinmu. Ba mu san abin da ya kamata mu roƙa cikin addu’a ba, amma Ruhu kansa yana roƙo a madadinmu da nishe-nishen da kalmomi ba sa iya bayyanawa.
27 And he who searches the hearts knows what is the mentality of the Spirit, because he appeals to God for the sanctified.
Shi kuma wanda yake binciken zukatanmu ya san halin Ruhu, domin Ruhu yana roƙo a madadin tsarkaka bisa ga nufin Allah.
28 And we know that all things work together for good to those who love God, who are the called according to purpose.
Mun kuma san cewa a cikin dukan abubuwa Allah yana aikata alheri ga waɗanda suke ƙaunarsa, yana waɗanda aka kira bisa ga nufinsa.
29 Because whom he foreknew, he also predestined to be of similar nature of the form of his Son, in order for him to be the firstborn son among many brothers.
Gama waɗanda Allah ya rigyasani ya kuma ƙaddara su dace da kamannin Ɗansa, don yă zama ɗan fari cikin’yan’uwa masu yawa.
30 And whom he predestined, these he also called, and whom he called, these he also made righteous, and whom he made righteous, these he also glorified.
Waɗanda kuwa ya ƙaddara, su ne ya kira; waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar; waɗanda ya kuɓutar kuwa, su ne ya ɗaukaka.
31 What then will we say to these things? If God is for us, who is against us?
Me za mu ce ke nan game da wannan abu? In Allah yana goyon bayanmu, wa kuwa zai iya gāba da mu?
32 He who did not even spare his own Son, but delivered him up for us all, how will he not also give us all things with him?
Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai kuma ba mu, tare da shi, dukan abubuwa cikin alherinsa ba?
33 Who will accuse against the chosen of God? God is he who makes righteous.
Wa zai kawo wani zargi a kan waɗanda Allah ya zaɓa? Allah ne mai kuɓutarwa.
34 Who is he who will condemn? It is Christ who died, but more, who also was raised up, who also is at the right hand of God, who also appeals for us.
Wa zai yi hukunci? Yesu Kiristi ne, wanda ya mutu, fiye da haka ma, shi da aka tā da zuwa rai, yana zaune a hannun dama na Allah yana kuma yin roƙo a madadinmu.
35 Who will separate us from the love of Christ? Will tribulation, or restriction, or persecution, or famine, or nakedness, or peril, or sword?
Wane ne zai raba mu da ƙaunar Kiristi? Masifa ce ko wahala ko tsanani ko yunwa ko tsiraici ko hatsari ko takobi?
36 Just as it is written, For thy sake we are killed the whole day long. We are considered as sheep of slaughter.
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Saboda kai ne muke fuskantar mutuwa dukan yini; an ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.”
37 But in all these things we are more than conquerors through him who loved us.
A’a, cikin dukan waɗannan abubuwa mun ma fi masu nasara ta wurin shi wanda ya ƙaunace mu.
38 For I am persuaded that neither death, nor life, nor agents, nor principal positions, nor powers, nor things that have come, nor things that are coming,
Gama na tabbata cewa ko mutuwa ko rai, ko mala’iku ko aljanu, ko abubuwa na yanzu ko abubuwa masu zuwa nan gaba, ko ikoki,
39 nor height, nor depth, nor any other creation, will be able to separate us from the love of God in Christ Jesus our Lord.
ko tsayi ko zurfi, ko wani abu dabam cikin dukan halitta da zai iya raba mu da ƙaunar Allah wadda take cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.

< Romans 8 >