< Romans 1 >

1 Paul, a bondman of Jesus Christ, a called apostle having been separated for the good news of God
Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
2 (which he fore-promised through his prophets in the holy scriptures)
Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
3 concerning his Son who was made from the seed of David according to flesh.
Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
4 He who was designated Son of God in power, according to a spirit of holiness, from a resurrection of the dead-Jesus Christ our Lord-
Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
5 through whom we received grace and apostleship for obedience of faith among all the nations on behalf of his name,
Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
6 among which ye also are the called of Jesus Christ.
cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7 To all who are in Rome, beloved of God, to the called, to the sanctified: Grace to you and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8 First, I indeed express thanks to my God through Jesus Christ for all of you, that your faith is proclaimed in the whole world.
Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
9 For God is my witness whom I serve in my spirit in the good news of his Son, how unceasingly I make mention of you always in my prayers,
Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
10 pleading, if somehow now at last I will have a prosperous journey by the will of God to come to you.
A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11 For I long to see you, so that I may impart some spiritual gift to you, in order to establish you,
Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
12 and that is, to be mutually encouraged among you through each other's faith, both yours and mine.
Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13 But I do not want you to be ignorant, brothers, that I often intended to come to you (and was prevented until now), so that I might have some fruit also among you, even as among the other Gentiles.
Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
14 I am debtor both to Greeks and to Barbarians, both to the wise and to the foolish.
Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
15 So the willingness is in me to preach the good news also to you in Rome.
Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16 For I am not ashamed of the good news of Christ, for it is the power of God for salvation to every man who believes, both to the Jew first, and to the Greek.
Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
17 For the righteousness of God is revealed in it from faith for faith, just as it is written, And the righteous man will live from faith.
Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
18 For the wrath of God is revealed from heaven against all irreverence and unrighteousness of men, who suppress the truth in unrighteousness,
Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
19 because what is knowable of God is apparent in them, for God made it known to them.
Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20 For the invisible things of him from the creation of the world are clearly seen, being understood by the things made, both his eternal power and divinity, for them to be without excuse. (aïdios g126)
Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios g126)
21 Because, although knowing God, they did not glorify him as God, nor were they thankful, but became vain in their reasonings and their heart was darkened without understanding.
Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22 Professing to be wise, they became foolish,
Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
23 and changed the glory of the incorruptible God into an image like corruptible man, and of birds, and four-footed things, and creeping things.
Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24 And for this reason God gave them up in the lusts of their hearts to uncleanness, to degrade their bodies among themselves,
Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
25 who changed the truth of God into the lie, and worshiped and served the creation against him who created it, who is blessed into the ages. Truly. (aiōn g165)
Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 Because of this God gave them up to shameful passions, for even their females changed the natural use into what is against nature.
Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
27 And likewise also the males, having left the natural use of the female, burned in their lust toward each other, males with males producing shamelessness, and receiving in themselves the recompense of their deviancy that was fitting.
Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28 And just as they did not approve having God in knowledge, God gave them over to an unfit mind, to do things that are not fit;
Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29 having been filled with all unrighteousness, fornication, wickedness, greed, evil; full of envy, murder, strife, deceit, malignity;
Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
30 being gossips, slanderous, God-hating, aggressors, arrogant boasters, contrivers of evil things, disobedient to parents;
Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
31 without understanding, untrustworthy, without natural affection, implacable, unmerciful.
Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32 Who, knowing the righteousness of God, that those who commit such things are worthy of death, not only do them, but also favor those who do.
Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.

< Romans 1 >