< Revelation 9 >

1 And the fifth agent sounded, and I saw a star fallen from the sky to the earth. And the key of the pit of the abyss was given to him. (Abyssos g12)
Sa'annan mala'ika na biyar ya busa kahonsa. Na ga tauraro daga sama da ya fado zuwa duniya. An ba tauraron nan mabudin hanyar rami marar iyaka. (Abyssos g12)
2 And he opened the pit of the abyss, and smoke ascended out of the pit, like smoke of a burning furnace. And the sun and the air were darkened from the smoke of the pit. (Abyssos g12)
Ya bude hanyar rami marar iyaka, sai hayaki ya fito daga kofar kamar hayaki daga babban ramin wuta. Rana da iska suka juya duhu, sabili da hayakin da ke fitowa daga kofar ramin. (Abyssos g12)
3 And locusts came forth out of the smoke upon the earth, and power was given to them, like the scorpions of the earth have power.
Daga cikin hayakin kuwa sai ga fari sun fito zuwa duniya, aka ba su iko kamar na kunamai cikin duniya.
4 And it was told them that they should not hurt the grass of the earth, nor anything green, nor any tree, except the men who have not the seal of God on their foreheads.
Aka gaya masu kada su yi wa ciyayi da kowanne koren ganye ko itace illa, sai dai mutanen da basu da hatimin Allah a goshinsu.
5 And it was given them that they would not kill them, but that they would be tormented five months. And their torment was as the torment of a scorpion when it strikes a man.
Ba a basu izini su kashe wadannan mutane ba, sai dai su azabtar da su na watani biyar. Zafinsu kuwa zai zama kamar na cizon kunama idan ta harbi mutum.
6 And in those days men will seek death, and will, no, not find it. And they will long to die, and death will flee from them.
A kwanakin nan mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba. Za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za ta guje su.
7 And the likeness of the locusts was similar to horses prepared for battle. And upon their heads were like golden crowns, and their faces were as men's faces.
Farin kuwa suna kama da dawakai da aka shirya domin yaki. A bisa kansu akwai wani abu kamar rawanan zinariya, fuskokinsu kuma kamar na 'yan adam.
8 And they had hair like the hair of women, and their teeth were as of lions.
Gashinsu kuma kamar na mata yake, hakoransu kamar hakoran zaki.
9 And they had breastplates like iron breastplates. And the sound of their wings was like the sound of chariots of many horses running into battle.
Sulkunansu kuma kamar na karfe, karar fikafikansu kuma kamar karar kekunan dawakin yaki masu yawa da dawakai da aka shirya domin zuwa yaki.
10 And they have tails similar to scorpions, and stings. And in their tails they have power to hurt men five months.
Suna da wutsiya da kari kamar kunamai; A wutsiyar su kuma suna da ikon da zai azabtar da mutane na tsawon wata biyar.
11 Having a king over them, the agent of the abyss, whose name in Hebrew is Abaddon, but in the Greek he has the name Apollyon. (Abyssos g12)
Suna da wani kamar sarki a kansu, mala'ikan rami marar iyaka. Sunansa da Ibraniyanci Abadon, da Helenanci kuma Afoliyon. (Abyssos g12)
12 One woe is departed, behold, two woes yet come after these.
Bala'i na fari ya wuce. Duba! Bayan wannan akwai masifu guda biyu masu zuwa.
13 And the sixth agent sounded, and I heard a voice, one from the four horns of the golden altar before God,
Mala'ika na shida ya busa kahonsa, sai na ji murya daga kahonin bagadin zinariya da ke gaban Allah.
14 saying to the sixth agent who has the trumpet, Loose the four agents who have been bound at the great river Euphrates.
Muryar ta ce wa mala'ika na shida da ke rike da kahon, “Kwance mala'ikun nan hudu da ke daure a babban kogin Yufiretis,''
15 And the four agents were loosed, who were prepared for the hour and for the day and month and year, so that they would kill the third part of men.
Mala'iku hudun da aka shirya domin wannan sa'a, da wannan rana, da wannan wata, da kuma wannan shekara, aka sake su su kashe daya bisa uku na 'yan adam.
16 And the number of the armies of the horsemen was ten thousands of ten thousands. I heard the number of them.
Yawan sojoji da ke kan dawakai shine 200, 000, 000. Na ji adadin su.
17 And thus I saw the horses in the vision, and those who sit on them having breastplates fiery red, and hyacinth color, and brimstone. And the heads of the horses are like heads of lions, and out of their mouths come fire and smoke and brimstone.
Haka na ga dawakan a cikin wahayina da mahayansu: Sulkunansu jawur kamar wuta, bakin shudi, da kuma ruwan doruwa. Kawunan dawakan suna kama da na zakuna, daga bakunansu kuma wuta, da hayaki da farar wuta suka fito.
18 By these three plagues the third part of men was killed, by the fire and the smoke and the brimstone coming out of their mouths.
Aka kashe daya bisa uku na mutane ta annoban nan uku: wuta, hayaki da farar wuta da suka fito daka bakunansu.
19 For the power of the horses is in their mouth, and in their tails. For their tails are similar to serpents, having heads, and by them they injure.
Domin iko na dawakan na bakunansu da wutsiyoyinsu - domin wutsiyoyinsu suna kama da macizai, kuma suna da kawuna wadanda dasu suke ji wa mutane rauni.
20 And the rest of the men who were not killed by these plagues, did not repent of the works of their hands, so that they would not worship the demons, and the golden and silver and brass and stone and wooden idols, which can neither see nor hear nor walk.
Sauran 'yan adam, da ba a kashe su ta wannan annoba ba, basu tuba daga ayyukan da suka yi ba. Basu kuma daina bautar aljanu da gumakan zinariya, da azurfa, da tagulla, da dutse, da itace ba - abubuwan da ba su gani, ji, ko tafiya.
21 And they did not repent of their murders, nor of their sorceries, nor of their fornication, nor of their thefts.
Basu kuma tuba ba daga kisan kai, sihiri, fasikanci, ko kuma ayyukansu na sata ba.

< Revelation 9 >