< Revelation 7 >
1 And after this I saw four agents standing at the four corners of the earth, restraining the four winds of the earth, so that wind would not blow on the earth, or on the sea, or upon any tree.
Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace.
2 And I saw another agent ascending from the rising of the sun, having a seal of the living God. And he cried out in a great voice to the four agents to whom it was given to them to harm the earth and the sea,
Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce,
3 saying, Do not harm the earth, nor the sea, nor the trees, until we may seal the bondmen of our God on their foreheads.
“Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.”
4 And I heard the number of those sealed, a hundred and forty-four thousand sealed out of every tribe of the sons of Israel.
Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.
5 Twelve thousand were sealed from the tribe of Judah, twelve thousand from the tribe of Reuben, twelve thousand from the tribe of Gad,
Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin, daga kabilar Ruben mutum 12,000, daga kabilar Gad mutum 12,000,
6 twelve thousand from the tribe of Asher, twelve thousand from the tribe of Naphtali, twelve thousand from the tribe of Manasseh,
daga kabilar Asher mutum 12,000, daga kabilar Naftali mutum 12,000, daga kabilar Manasse mutum 12,000,
7 twelve thousand from the tribe of Simeon, twelve thousand from the tribe of Levi, twelve thousand from the tribe of Issachar,
daga kabilar Simeyon mutum 12,000, daga kabilar Lawi mutum 12,000, daga kabilar Issakar mutum 12,000,
8 twelve thousand from the tribe of Zebulun, twelve thousand from the tribe of Joseph, twelve thousand from the tribe of Benjamin, were sealed.
daga kabilar Zebulun mutum 12,000, daga kabilar Yusuf mutum 12,000, daga kabilar Benyamin mutum 12,000.
9 After these things, I looked and lo, a great multitude, which none could number, out of every nation, and tribes and peoples and tongues, standing before the throne and before the Lamb, clothed in white robes, and palms in their hands,
Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu.
10 and crying out in a great voice, saying, Salvation is in our God who sits upon the throne, and in the Lamb!
Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa, “Ceto na Allahnmu ne, wanda yake zaune a bisan kursiyi, da kuma na Ɗan Ragon.”
11 And all the agents had stood all around the throne, and the elders, and the four living creatures, and they fell before his throne on their faces, and worshiped God,
Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada,
12 saying, Truly! Blessing, and glory, and wisdom, and thanksgiving, and honor, and power, and strength, is for our God into the ages of the ages. Truly! (aiōn )
suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn )
13 And one of the elders answered, saying to me, Who are these who are clothed in white robes, and where did they come from?
Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”
14 And I said to him, My lord, thou know. And he said to me, These are those coming out of the great tribulation, and they washed their robes, and made them white in the blood of the Lamb.
Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.” Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan.
15 Because of this they are before the throne of God, and they serve him day and night in his temple. And he who sits on the throne will dwell among them.
Saboda haka, “suna a gaban kursiyin Allah suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa; kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.
16 They will hunger no more, nor will they thirst any more. The sun will, no, not fall upon them, nor any heat.
‘Ba za su sāke jin yunwa ba; ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba. Rana ba za tă buga su ba,’ ko kuma kowane irin zafin ƙuna.
17 Because the Lamb in the midst of the throne will tend them, and will lead them to fountains of waters of life. And God will wipe away every tear from their eyes.
Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu; ‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’ ‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’”