< Revelation 5 >
1 And I saw at the right hand of him who sits on the throne a book, written inside and outside, sealed with seven seals.
Sa'annan na ga a cikin hannun daman wanda ke zaune a kan kursiyin, na ga littafi wanda ke da rubutu ciki da waje, an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
2 And I saw a powerful agent proclaiming in a great voice, Who is worthy to open the book, and to loose the seals of it?
Na kuma ga wani kakkarfan mala'ika na shela da murya mai karfi, “Wa ya isa ya bude littafin ya kuma bambare hatimin?”
3 And none in heaven above nor on the earth nor under the earth was able to open the book or to see in it.
Ba wani a sama ko a kasa ko karkashin kasa da ya iya ya bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa.
4 And I wept much because none was found worthy to open the book or to see in it.
Na yi kuka mai zafi saboda ba wani da ya cancanta da zai bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa.
5 And one of the elders says to me, Weep not, behold, the Lion of the tribe of Judah, the Root of David, overcame to open the book and the seven seals of it.
Amma daya daga cikin dattawan nan ya ce mani, “Kada ka yi kuka. Duba! Zaki na kabilar Yahuza, Tushen Dauda, ya yi nasara. Ya cancanci bude littafin da kuma hatimansa bakwai.”
6 And I saw in the midst of the throne and of the four living creatures, and in the midst of the elders, a Lamb standing, like it had been killed, having seven horns and seven eyes, which are the seven Spirits of God being sent forth into all the earth.
Na ga Dan Rago yana tsaye tsakanin kursiyin da rayayyun halittun nan guda hudu a cikin dattawa. Yana kama da wanda aka kashe. Yana da kafonni bakwai da idanuwa bakwai; wadannan sune ruhohin Allah bakwai da aka aiko zuwa dukan duniya.
7 And he came and took it out of the right hand of him who sits on the throne.
Ya tafi ya karbi littafin daga hannun daman wanda ke zaune bisa kursiyin.
8 And when he took the book, the four living creatures and the twenty-four elders fell down before the Lamb, each having a harp and golden bowls containing incense, which are the prayers of the sanctified.
Lokacin da Dan Ragon ya dauki littafin, rayayyun halittun nan hudu da dattawan nan ashirin da hudu suka fadi har kasa a gaban Dan ragon. Kowannen su na dauke da molo da tasar zinariya cike da kayan kamshi, wadanda kuwa sune addu'o'in masu ba da gaskiya.
9 And they sing a new song, saying, Thou are worthy to take the book and to open the seals of it, because thou were killed and purchased us from God by thy blood, out of every tribe, and tongue, and people, and nation.
Suka raira sabuwar waka: “Ka cancanta ka dauki littafinka kuma bude hatimansa. Domin an yanka ka, da jininka ka saya wa Allah mutane daga kowacce kabila, harshe, jama'a da al'umma.
10 And thou made them kings and priests to our God, and they will reign over the earth.
Ka maishe su mulki da firistoci su bauta wa Allanmu, kuma za su yi mulki a duniya.”
11 And I looked, and I heard as a voice of many agents all around the throne and the living creatures and the elders. And the number of them was ten thousands of ten thousands, and thousands of thousands,
Da na duba sai na ji karar mala'iku masu yawa kewaye da kursiyin da rayayyun halitu da kuma dattawa. Jimillarsu ya kai dubbai goma, sau dubbai goma, da dubun dubbai.
12 saying with a great voice, Worthy is the Lamb that has been killed to receive the power, and wealth, and wisdom, and strength, and honor, and glory, and blessing!
Suka tada murya da karfi suka ce, “Macancanci ne Dan Ragon da aka yanka ya karbi iko, wadata, hikima, karfi, girma, daukaka da yabo.”
13 And every creature that is in the heaven, and on the earth, and under the earth, and is in the sea, and things in them all, I heard saying, The blessing, and the honor, and the glory, and the dominion is to him who sits upon the throne, and to the Lamb, into the ages of the ages. Truly! (aiōn )
Na ji kowanne halittaccen abu da ke cikin sama da kasa da karkashin kasa da cikin teku - dukan abubuwan da ke cikinsu - na cewa, “Ga shi wanda ke zaune a kan kursiyin da kuma Dan Ragon, yabo, girma, daraja, da kuma ikon yin mulki, har abada abadin. (aiōn )
14 And the four living creatures were saying the Truly. And the elders fell down and worshiped.
Sai rayayyun halittun nan hudu suka ce, “Amin!” dattawan nan kuma suka fadi da fuskokinsu suka yi sujada.