< Revelation 21 >

1 And I saw a new heaven and a new earth, for the first heaven and the first earth passed away, and the sea is no more.
Sa’an nan na ga sabon sama da sabuwar duniya, gama sama na farko da duniya ta farko sun shuɗe, babu kuma wani teku.
2 And I saw the holy city, new Jerusalem, coming down out of heaven from God, having been prepared as a bride adorned for her husband.
Na ga Birni Mai Tsarki, sabuwar Urushalima tana saukowa daga sama, daga Allah, a shirye kamar amaryar da aka yi mata ado mai kyau saboda mijinta.
3 And I heard a great voice out of heaven saying, Behold, the tabernacle of God is with men, and he will dwell with them, and they will be his people. And God himself will be with them.
Na kuma ji wata babbar murya daga kursiyin tana cewa, “Yanzu mazaunin Allah yana tare da mutane, zai kuma zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kansa kuwa zai kasance tare da su yă kuma zama Allahnsu.
4 And he will wipe away every tear from their eyes. And there will not be any more death, nor grief, nor crying, nor will there be any more anguish, because the former things are gone.
Zai share dukan hawaye daga idanunsu. Ba sauran mutuwa ko makoki ko kuka ko azaba, gama tsofaffin al’amura sun shuɗe.”
5 And he who sits upon the throne said, Behold, I make all things new. And he says to me, Write, because these words are true and faithful.
Wannan da yake zaune a kursiyin ya ce. “Ina yin kome sabo!” Sai ya ce, “Rubuta wannan, domin waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma.”
6 And he said to me, I have become, I, the Alpha and the Omega, the beginning and the end. I will give to him who is thirsty of the fountain of the water of life freely.
Ya ce mini, “An gama. Ni ne Alfa da kuma Omega, na Farko da kuma na Ƙarshe. Duk mai jin ƙishirwa zan ba shi abin sha kyauta daga maɓulɓular ruwan rai.
7 He who overcomes will inherit these things, and I will be God to him, and he will be a son to me.
Duk wanda ya ci nasara zai gāji dukan wannan, zan kuma zama Allahnsa, shi kuma zai zama ɗana.
8 But for the cowards, and unbelieving, and sinful, and abominable, and murderers, and fornicators, and sorcerers, and idolaters, and all liars, their part is in the lake that burns with fire and brimstone, which is the second death. (Limnē Pyr g3041 g4442)
Amma matsorata, da marasa bangaskiya, masu ƙazanta, masu kisankai, masu fasikanci, masu sihiri, masu bautar gumaka da dukan maƙaryata, wurinsu zai kasance a cikin tafkin wutar da yake farar wuta mai ci. Wannan fa ita ce mutuwa ta biyu.” (Limnē Pyr g3041 g4442)
9 And there came one of the seven agents who had the seven bowls containing the seven last plagues, and he spoke with me, saying, Come, I will show thee the woman, the bride of the Lamb.
Ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai masu kwanonin nan bakwai cike da annoban nan bakwai na ƙarshe, ya zo ya ce mini “Zo, zan nuna maka amaryar, matar Ɗan Ragon.”
10 And he carried me away in spirit to a great and high mountain, and showed me the great city, holy Jerusalem, coming down out of heaven from God,
Ya kuwa ɗauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsayi, ya kuma nuna mini Birni Mai Tsarki, Urushalima, tana saukowa daga sama, daga Allah.
11 having the glory of God, the light of it similar to a most precious stone, like a jasper stone being crystal clear,
Ya haskaka da ɗaukakar Allah, haskensa kuwa ya yi kamar lu’ulu’u mai daraja sosai, kamar yasfa, yana ƙyalƙyali kamar madubi.
12 which has a great and high wall having twelve gates, and at the gates twelve agents, and names inscribed, which are the names of the twelve tribes of the sons of Israel:
Yana da babbar katanga mai tsayi, mai ƙofofi goma sha biyu, da kuma mala’iku goma sha biyu a ƙofofin. A bisa ƙofofin an rubuta sunayen kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
13 from the east, three gates, and from the north, three gates, and from the south, three gates, and from the west, three gates.
Akwai ƙofofi uku a gabas, uku a arewa, uku a kudu, uku kuma a yamma.
14 And the wall of the city having twelve foundations, and on them the twelve names of the twelve apostles of the Lamb.
An gina katangar birnin a kan tushen gini goma sha biyu, a kansu kuwa akwai sunayen manzannin sha biyu na Ɗan Ragon.
15 And he who spoke with me had a measure, a golden reed, so that he might measure the city, and the gates of it, and the walls of it.
Mala’ikan da ya yi magana da ni yana da sandan awo na zinariya don awon birnin, ƙofofinsa, da kuma katangarsa.
16 And the city lies foursquare, and the length of it is as great as the breadth. And he measured the city with the reed, twelve thousand furlongs, the length and the breadth and the height of it being equal.
Birnin murabba’i ne, tsayinsa daidai ne da fāɗinsa. Ya auna birnin da sandarsa ya kuwa sami mil 1,400 (wajen kilomita 2,200) tsawonsa, fāɗinsa da kuma tsayinsa daidai suke.
17 And he measured the wall of it, a hundred and forty-four forearms, a measure of a man, that is, of an agent.
Ya auna katangarsa ya kuma sami ƙaurinta kamun 144, bisa ga ma’aunin mutum, wanda mala’ikan ya yi amfani da shi.
18 And the structure of its wall was jasper. And the city was pure gold, similar to clear glass.
An yi katangar da yasfa, birnin kuma da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.
19 And the foundations of the wall of the city adorned with every precious stone. The first foundation was jasper, the second, sapphire, the third, chalcedony, the fourth, emerald,
Tushen ginin katangar birnin kuwa an yi masa adon da kowane irin dutse mai daraja. Tushe na farko an yi shi yasfa, na biyu saffaya, na uku agat, na huɗu zumurrudu,
20 the fifth, sardonyx, the sixth, sardius, the seventh, chrysolite, the eighth, beryl, the ninth, topaz, the tenth, chrysoprase, the eleventh, jacinth, the twelfth, amethyst.
na biyar onis, na shida yakutu, na bakwai kirisolit, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofuras, na goma sha ɗaya yasin, na goma sha biyu kuma ametis.
21 And the twelve gates were twelve pearls apiece, each one of the gates was of one pearl. And the thoroughfare of the city was pure gold, like transparent glass.
Ƙofofi goma sha biyun nan lu’ulu’ai goma sha biyu ne, kowace ƙofa an yi ta da lu’ulu’u guda. Babban titin birnin kuwa an yi shi da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.
22 And I saw no temple in it, for the Lord God Almighty is the temple of it, and the Lamb.
Ban ga haikali a cikin birnin ba, domin Ubangiji Allah Maɗaukaki da kuma Ɗan Ragon ne haikalin birnin.
23 And the city has no need of the sun, nor of the moon, so that they might shine in it, for the glory of God illuminated it, and the light of it is the Lamb.
Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, gama ɗaukakar Allah tana ba shi haske, Ɗan Ragon kuwa shi ne fitilar birnin.
24 And the nations will walk by the light of it. And the kings of the earth bring to them the splendor and worth of the nations into it.
Al’ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin, sarakunan duniya kuma za su kawo darajarsu cikin birnin.
25 And the gates of it will, no, not be locked by day, for there will be no night there.
Ba za a taɓa rufe ƙofofin birnin da rana ba, gama ba za a yi dare a can ba.
26 And they will bring the splendor and the worth of the nations into it.
Za a kawo ɗaukaka da girmar al’ummai a cikin birnin.
27 And there will, no, not enter into it anything profane, and doing an abomination and a lie, since they are not written in the Lamb's book of life.
Babu wani abu marar tsarkin da zai taɓa shiga cikin birnin, babu kuma wani mai aikata abin kunya ko ruɗi da zai shiga, sai dai waɗanda aka rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Ɗan Ragon.

< Revelation 21 >