< Revelation 19 >
1 And after these things I heard as a great sound of a large multitude in heaven, saying, Praise the Lord, the salvation, and the power, and the glory of our God!
Bayan wannan sai na ji abin da ya yi kamar ƙasaitaccen taron mutane a sama, suna cewa, “Halleluya! Ceto da ɗaukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu,
2 Because true and righteous are his judgments, because he has judged the great whore who ruined the earth by her fornication, and he has avenged the blood of his bondmen from her hand.
gama hukuncinsa daidai ne, mai adalci kuma. Ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta ɓata duniya da zinace zinacenta. Ya rama jinin bayinsa a kanta.”
3 And a second time they said, Praise the Lord! And the smoke of her ascended into the ages of the ages. (aiōn )
Suka sāke tā da murya suka ce, “Halleluya! Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin.” (aiōn )
4 And the twenty-four elders and the four living creatures fell down and worshiped God who sits on the throne, saying, Truly! Praise the Lord!
Dattawan nan ashirin da huɗu da halittu huɗun nan masu rai suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, wannan da yake zaune a kursiyi. Suka tā da murya suka ce, “Amin, Halleluya!”
5 And a voice came forth from the throne, saying, Praise ye our God, all his bondmen and those who fear him, the small and the great.
Sa’an nan wata murya ta fito daga kursiyin, tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, dukanku da kuke bayinsa, ku da kuke tsoronsa, babba da yaro!”
6 And I heard as the sound of a large multitude, and as the sound of many waters, and as the sound of mighty thunders, saying, Praise the Lord! Because the Lord our God, the Almighty, reigns.
Sai na ji wani abu mai ƙara kamar ƙasaitaccen taron mutane, kamar rurin ruwaye masu gudu da kuma kamar bugun tsawa mai ƙarfi, suna tā da murya suna cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu Maɗaukaki ne yake mulki.
7 We should be glad and rejoice and give the glory to him, because the marriage of the Lamb has come, and his wife has prepared herself.
Bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna mu kuma ɗaukaka shi! Domin lokacin auren Ɗan Ragon ya yi, amaryarsa kuwa ta shirya kanta.
8 And it was given her that she clothe herself in fine linen, bright and pure. For the fine linen is the righteous deeds of the sanctified.
Aka ba ta lallausan lilin, mai haske da tsabta ta sanya.” (Lallausan lilin yana misalta ayyukan adalci na tsarkaka.)
9 And he says to me, Write, Blessed are those who have been called to the supper of the marriage of the Lamb. And he says to me, These are the true sayings of God.
Sai mala’ikan ya ce mini, “Rubuta, ‘Masu albarka ne waɗanda aka gayyace su zuwa bikin auren Ɗan Ragon!’” Sai ya ƙara da cewa, “Waɗannan su ne kalmomin Allah da gaske.”
10 And I fell down before his feet to worship him. And he says to me, See thou not. I am a fellow bondman of thee and thy brothers, those who have the testimony of Jesus. Worship God, for the testimony of Jesus is the spirit of prophecy.
Da wannan sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada. Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne da kai da kuma’yan’uwanka waɗanda suke riƙe da shaidar Yesu. Ka yi wa Allah sujada! Domin shaidar Yesu ita ce ruhun annabci.”
11 And I saw the heaven opened, and behold a white horse, and he who sits upon it called Faithful and True, and in righteousness he judges and makes war.
Sai na ga sama a buɗe can kuwa a gabana ga farin doki, sunan mahayinsa Mai Aminci da Mai Gaskiya ne. Da adalci yake shari’a yake kuma yaƙi.
12 And his eyes are a flame of fire, and upon his head are many diadems having names written, and a name written that none knows except he himself,
Idanunsa sun yi kamar harshen wuta, a kansa kuwa akwai rawani masu yawa. Yana da suna rubuce a kansa da babu wanda ya sani sai dai shi.
13 and clothed in a garment dipped in blood. And his name is called The Word of God.
Yana saye da rigar da aka tsoma a jini, sunansa kuwa Kalman Allah ne.
14 And the armies in heaven followed him upon white horses, clothed in fine linen, pure white.
Mayaƙan sama suna biye da shi, suna hawan fararen dawakai, saye da fararen tufafi masu tsabta na lallausan lilin.
15 And a sharp two-edged sword comes out of his mouth, so that he would smite the nations by it. And he will tend them with a rod of iron. And he treads the winepress of the wine of the wrath of the anger of the Almighty God.
Daga bakinsa takobi mai kaifi ya fito. Da shi zai karkashe al’ummai. “Zai yi mulkinsu da sandan sarautar ƙarfe.” Yana tattake wurin matsin ruwan inabi na fushin Allah Maɗaukaki.
16 And he has on his garment and on his thigh a name written, KING OF KINGS AND LORD OF LORDS.
A rigarsa da kuma a cinyarsa akwai wannan suna a rubuce, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji.
17 And I saw one agent having stood in the sun, and he cried out in a great voice, saying to all the birds flying in mid-heaven, Come, gather together to the great supper of God,
Na kuma ga wani mala’ika tsaye a cikin rana, wanda ya yi kira da babbar murya ga dukan tsuntsaye da suke tashi sama a tsakiyar sararin sama cewa, “Ku zo, ku taru don babban bikin nan na Allah,
18 so that ye may eat the flesh of kings, and the flesh of captains, and the flesh of mighty men, and the flesh of horses and of those who sit upon them, and the flesh of all men, both freemen and bondmen, and both small and great.
don ku ci naman sarakuna, jarumawa, da kuma manyan mutane, na dawakai da mahayansu, da kuma naman dukan mutane,’yantacce da bawa, babba da yaro.”
19 And I saw the beast, and the kings of the earth, and their armies gathered together to make war against him who sits upon the horse, and against his army.
Sa’an nan na ga dabbar da sarakunan duniya da mayaƙansu sun taru don su yi yaƙi da wannan wanda yake kan farin dokin da kuma mayaƙansa.
20 And the beast was taken, and the false prophet with it who did the signs in its sight by which he led astray those who received the mark of the beast and those who worship its image. The two were thrown alive into the lake of fire that burns with brimstone. (Limnē Pyr )
Amma aka kama dabbar tare da annabin ƙaryan nan wanda ya aikata alamu masu banmamaki a madadinta. Da waɗannan alamun ne ya ruɗe waɗanda suka sami alamar dabbar suka kuma bauta wa siffarta. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin wuta ta da farar wuta mai ci. (Limnē Pyr )
21 And the others were killed by the sword that comes forth out of his mouth (of him who sits upon the horse), and all the birds were filled from their flesh.
Sauran kuma aka kashe su da takobin da ya fito daga bakin wannan wanda yake kan dokin. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu iyakar iyawarsu.