< Psalms 88 >
1 O Jehovah, the God of my salvation, I have cried day and night before thee.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Let my prayer enter into thy presence. Incline thine ear to my cry.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 For my soul is full of troubles, and my life draws near to Sheol. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 I am reckoned with those who go down into the pit. I am as a man who has no help,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 cast off among the dead, like the slain who lie in the grave, whom thou remember no more, and they are cut off from thy hand.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Thou have laid me in the lowest pit, in dark places, in the deeps.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Thy wrath lays hard upon me, and thou have afflicted me with all thy waves. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Thou have put my acquaintances far from me. Thou have made me an abomination to them. I am shut up, and I cannot come forth.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 My eye wastes away because of affliction. I have called daily upon thee, O Jehovah, I have spread forth my hands to thee.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Will thou show wonders to the dead? Shall those who are deceased arise and praise thee? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Shall thy loving kindness be declared in the grave, or thy faithfulness in destruction?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Shall thy wonders be known in the dark, and thy righteousness in the land of forgetfulness?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 But to thee, O Jehovah, I have cried, and in the morning my prayer shall come before thee.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Jehovah, why do thou cast off my soul? Why do thou hide thy face from me?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 I am afflicted and ready to die from my youth up. While I suffer thy terrors I am confounded.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Thy fierce wrath has gone over me. Thy terrors have cut me off.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 They came round about me like water all the day long. They encompassed me around together.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Thou have put beloved and friend far from me, and my acquaintances into darkness.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.