< Psalms 49 >
1 Hear this, all ye peoples. Give ear, all ye inhabitants of the world,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 both low and high, rich and poor together.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 My mouth shall speak wisdom, and the meditation of my heart shall be of understanding.
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 I will incline my ear to a proverb. I will open my dark saying upon the harp.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Why should I fear in the days of evil, when iniquity at my heels encompasses me about?
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 Those who trust in their wealth, and boast themselves in the multitude of their riches,
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 none can by any means redeem his brother, nor give to God a ransom for him
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 (for the redemption of their life is costly, and it fails forever),
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 that he should still live always, that he should not see corruption.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 For he shall see it. Wise men die. The fool and the brutish alike perish, and leave their wealth to others.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 Their inward thought is that their houses are forever, their dwelling-places to all generations. They call their lands after their own names.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 Even a man in splendor does not abide. He is like the beasts that perish.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 This their way is their folly. Yet after them men approve their sayings. (Selah)
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 They are appointed as a flock for Sheol. Death shall be their shepherd, and the upright shall have dominion over them in the morning. And their beauty shall be for Sheol to consume, that there be no habitation for it. (Sheol )
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
15 But God will redeem my soul from the power of Sheol, for he will receive me. (Selah) (Sheol )
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
16 Be not thou afraid when a man is made rich, when the glory of his house is increased.
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 For when he dies he shall carry nothing away. His glory shall not descend after him.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 Though while he lived he blessed his soul (and men praise thee, when thou do well for thyself),
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 he shall go to the generation of his fathers. They shall never see the light.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 A man who is in splendor, and understands not, is like the beasts that perish.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.