< Psalms 30 >
1 I will extol thee, O Jehovah, for thou have raised me up, and have not made my foes to rejoice over me.
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 O Jehovah my God, I cried to thee, and thou have healed me.
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3 O Jehovah, thou have brought up my soul from Sheol. Thou have kept me alive, that I should not go down to the pit. (Sheol )
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol )
4 Sing praise to Jehovah, O ye sanctified of his, and give thanks to his holiness.
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5 For his anger is but for a moment. His favor is for a lifetime. Weeping may tarry for the night, but joy is in the morning.
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
6 As for me, I said in my prosperity, I shall never be moved.
Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
7 Thou, Jehovah, of thy favor had made my mountain to stand strong. Thou hid thy face; I was troubled.
Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
8 I cried to thee, O Jehovah, and to Jehovah I made supplication.
A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
9 What profit is there in my blood when I go down to the pit? Shall the dust praise thee? Shall it declare thy truth?
“Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
10 Hear, O Jehovah, and have mercy upon me. Jehovah, be thou my helper.
Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
11 Thou have turned for me my mourning into dancing. Thou have loosed my sackcloth, and girded me with gladness,
Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
12 to the end that my glory may sing praise to thee, and not be silent. O Jehovah my God, I will give thanks to thee forever.
don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.