< Micah 5 >
1 Now thou shall gather thyself in troops, O daughter of troops. He has laid siege against us. They shall smite the judge of Israel with a rod upon the cheek.
Ki tattara sojojinki, ya ke birnin mayaƙa, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun mai mulkin Isra’ila da sandar ƙarfe.
2 But thou, Bethlehem Ephrathah, which are little to be among the thousands of Judah, out of thee he shall come forth to me who is to be ruler in Israel, whose goings forth are from of old, from everlasting.
“Amma ke, Betlehem ta Efrata, ko da yake ke ƙarama ce daga cikin zuriyarki a Yahuda, daga cikinki wani zai zo domina wanda zai yi mulkin Isra’ila, wanda asalinsa tun fil azal ne.”
3 Therefore he will give them up until the time that she who travails has brought forth. Then the residue of his brothers shall return to the sons of Israel.
Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.
4 And he shall stand, and shall feed his flock in the strength of Jehovah, in the majesty of the name of Jehovah his God, and they shall abide. For now he shall be great to the ends of the earth.
Zai tsaya yă yi kiwon garkensa da ƙarfin Ubangiji, cikin girman sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuma zauna lafiya, gama girmansa za tă kai har ƙarshen duniya.
5 And this man shall be our peace. When the Assyrian shall come into our land, and when he shall tread in our palaces, then we shall raise against him seven shepherds, and eight principal men.
Zai kuma zama salamarsu. Sa’ad da Assuriyawa suka kawo wa ƙasarmu hari suka tattake kagarunmu, za mu tā da makiyaya bakwai, har ma shugabannin mutane takwas su yi gāba da su.
6 And they shall waste the land of Assyria with the sword, and the land of Nimrod in the entrances of it. And he shall deliver us from the Assyrian, when he comes into our land, and when he treads within our border.
Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
7 And the remnant of Jacob shall be in the midst of many peoples as dew from Jehovah, as showers upon the grass, that tarry not for man, nor wait for the sons of men.
Raguwar Yaƙub za tă kasance a tsakiyar mutane masu yawa kamar raɓa daga Ubangiji, kamar yayyafi a kan ciyawa, wanda ba ya jiran mutum ko kuma yă dakata wa ɗan adam.
8 And the remnant of Jacob shall be among the nations, in the midst of many peoples, as a lion among the beasts of the forest, as a young lion among the flocks of sheep, who, if he goes through, treads down and tears in pieces, and there is none to deliver.
Raguwar Yaƙub za tă kasance tare da al’ummai, a cikin mutane masu yawa, kamar zaki a cikin sauran namun jeji, kamar ɗan zaki cikin garken tumaki, wanda yake tattaka yă kuma yi kaca-kaca da su sa’ad da yake ratsa a cikinsu, ba kuwa wanda zai cece su.
9 Let thy hand be lifted up above thine adversaries, and let all thine enemies be cut off.
Za a ɗaga hannunka cikin nasara a kan abokan gābanka, za a hallaka maƙiyanka duka.
10 And it shall come to pass in that day, says Jehovah, that I will cut off thy horses out of the midst of thee, and will destroy thy chariots,
“A wannan rana,” in ji Ubangiji “Zan hallaka dawakanku daga cikinku, in kuma rurrushe kekunan yaƙinku.
11 and I will cut off the cities of thy land, and will throw down all thy strongholds.
Zan hallaka biranen ƙasarku in yi rugu-rugu da dukan katangunku.
12 And I will cut off witchcrafts out of thy hand, and thou shall have no more soothsayers.
Zan kawar da maitarku, ba za a ƙara yin sihiri ba.
13 And I will cut off thy graven images and thy pillars out of the midst of thee, and thou shall no more worship the work of thy hands.
Zan sassare dukan gumakan da kuka sassaƙa da keɓaɓɓun duwatsunku a cikinku, nan gaba ba za ku ƙara rusuna wa aikin hannuwanku ba.
14 And I will pluck up thine Asherim out of the midst of thee, and I will destroy thy cities.
Zan tumɓuke daga gare ku ginshiƙan Asheranku in kuma rurrushe biranenku.
15 And I will execute vengeance in anger and wrath upon the nations that did not hearken.
Zan yi ramuwa cikin fushi da hasala a kan al’umman da ba su yi mini biyayya ba.”