< Matthew 2 >
1 Now Jesus having been born in Bethlehem of Judea in the days of Herod the king, behold, wise men from the east came to Jerusalem, saying,
Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
2 Where is he who is born king of the Jews? For we saw his star in the east, and have come to worship him.
suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
3 And Herod the king having heard it, he was troubled, and all Jerusalem with him.
Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
4 And having gathered together all the chief priests and scholars of the people, he inquired of them where the Christ is born.
Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
5 And they said to him, In Bethlehem of Judea. For thus it is written through the prophet,
Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
6 And thou Bethlehem, land of Judah, are in no way least among the rulers of Judah, for out of thee will come forth a man who rules, who will tend my people Israel.
“‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
7 Then Herod having called the wise men privately, ascertained from them what time the star appeared.
Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
8 And having sent them to Bethlehem, he said, After going, search diligently about the child. And when ye find him, report to me, so that I also having come, may worship him.
Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
9 And when they heard the king, they departed. And lo, the star that they saw in the east went before them until, having come, it stood over where the child was.
Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
10 And when they saw the star, they rejoiced with exceedingly great joy.
Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
11 And having come into the house, they saw the child with Mary his mother, and having fallen down, they worshiped him. And having opened their treasures, they brought to him gifts, gold and frankincense and myrrh.
Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
12 And divinely warned in a dream not to return to Herod, they departed into their own country by another way.
Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
13 Now after they departed, behold, an agent of the Lord appears to Joseph in a dream, saying, After rising, take the child and his mother, and flee into Egypt, and thou be there until I tell thee, for Herod is going to seek the child to destroy it.
Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
14 And having awakened, he took the child and his mother by night, and departed into Egypt.
Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
15 And he was there until the end of Herod, so that what was spoken by the Lord through the prophet might be fulfilled, which says, Out of Egypt I called my Son.
inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
16 Then Herod, when he saw that he was scorned by the wise men, was exceedingly angry, and having sent forth, he killed all the boys in Bethlehem, and in all the borders of it, from two years old and under, according to the time that he had ascertained from the wise men.
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
17 Then that which was spoken through Jeremiah the prophet was fulfilled, which says,
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
18 A voice was heard in Ramah, lamentation, and weeping, and great mourning, Rachel weeping for her children. And she did not want to be comforted, because they are not.
“An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
19 But when Herod perished, behold, an agent of the Lord appears in a dream to Joseph in Egypt, saying,
Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
20 After rising, take the child and his mother, and go into the land of Israel, for those seeking the child's life have died.
ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
21 And having awaken, he took the child and his mother, and came into the land of Israel.
Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
22 But when he heard that Archelaus was reigning over Judea in place of his father Herod, he was afraid to go there. And divinely warned in a dream, he withdrew into the parts of Galilee.
Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
23 And having come, he dwelt in a city called Nazareth, so that what was spoken through the prophets might be fulfilled, that he will be called a Nazarene.
ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”