< Matthew 17 >

1 And after six days Jesus takes Peter, and James, and John his brother, and brings them up onto a high mountain in private.
Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus da Yakubu, da Yahaya dan'uwansa, ya kai su kan wani dutse mai tsawo su kadai.
2 And he was transfigured before them, and his face shone as the sun, and his garments became white as the light.
Kamanninsa ya canja a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, kuma rigunansa suka yi kyalli fal.
3 And behold, Moses and Elijah appeared to them, talking with him.
Sai ga Musa da Iliya sun bayyana garesu suna magana da shi.
4 And having responded, Peter said to Jesus, Lord, it is good for us to be here. If thou desire, we could make here three tabernacles, one for thee, and one for Moses, and one for Elijah.
Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke a wurin nan. In kana so, zan yi bukkoki uku daya dominka, daya domin Musa, daya domin Iliya.”
5 While he was still speaking, behold, a bright cloud overshadowed them. And lo, a voice out of the cloud, saying, This is my beloved Son in whom I am well pleased. Hear ye him.
Sa'adda yake cikin magana, sai, girgije mai haske ya rufe su, sai murya daga girgijen, tana cewa, “Wannan kaunattacen Dana ne, shi ne wanda yake faranta mani zuciya. Ku saurare shi.”
6 And when the disciples heard it, they fell on their face, and were exceedingly afraid.
Da almajiran suka ji haka, suka fadi da fuskokinsu a kasa, saboda sun tsorata.
7 And having come, Jesus touched them and said, Arise, and fear not.
Sai Yesu ya zo ya taba su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
8 And having lifted up their eyes, they saw no man, except Jesus only.
Amma da suka daga kai ba su ga kowa ba sai Yesu kadai.
9 And while they were coming down from the mountain, Jesus commanded them, saying, Tell the vision to no man, until the Son of man will rise from the dead.
Yayin da suke saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su, ya ce, “Kada ku fadawa kowa wannan wahayin, sai Dan Mutum ya tashi daga matattu.”
10 And his disciples questioned him, saying, Why then do the scholars say that Elijah must first come?
Almajiransa suka tambaye shi, suka ce, “Don me marubuta ke cewa lallai ne Iliya ya fara zuwa?”
11 And having answered, Jesus said to them, Elijah indeed comes first, and will restore all.
Yesu ya amsa ya ce, “Hakika, Iliya zai zo ya maido da dukan abubuwa.
12 But I say to you, that Elijah already came, and they knew him not, but did to him how many things they wanted. Likewise also the Son of man is going to suffer by them.
Amma ina gaya maku, Iliya ya riga ya zo, amma ba su gane shi ba. A maimakon haka, suka yi masa abin da suka ga dama. Ta irin wanan hanya, Dan Mutum kuma zai sha wuya a hannunsu.
13 Then the disciples understood that he spoke to them about John the immerser.
Sa'annan almajiransa suka fahimci cewa yana yi masu magana a kan Yahaya mai Baftisma ne.
14 And when they came to the multitude, a man came to him, kneeling to him, and saying,
Da suka iso wurin taron, wani mutum ya zo gunsa, ya durkusa a gaban sa, ya ce,
15 Lord, be merciful to my son, because he is lunatic, and suffers badly. For he often falls into the fire, and often into the water.
“Ubangiji, ka ji tausayin yarona, domin yana da farfadiya, kuma yana shan wuya kwarai, domin sau da yawa yana fadawa cikin wuta ko ruwa.
16 And I brought him to thy disciples, and they could not heal him.
Na kawo shi wurin almajiran ka, amma ba su iya su warkar da shi ba.”
17 And having answered, Jesus said, O faithless and perverted generation, how long will I be with you? How long will I endure you? Bring him here to me.
Yesu ya amsa ya ce, “Marasa bangaskiya da karkataccen zamani, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan jure da ku? Ku kawo shi nan a wurina.”
18 And Jesus rebuked it, and the demon departed from him. And the boy was cured from that hour.
Yesu ya tsauta masa, sai aljanin ya fita daga cikinsa. Yaron ya warke nan take.
19 Then the disciples having come to Jesus in private, said, Why could we not cast it out?
Sai almajiran suka zo wurin Yesu a asirce suka ce, “Me ya sa muka kasa fitar da shi?”
20 And Jesus said to them, Because of your unbelief. For truly I say to you, if ye have faith as a grain of a mustard plant, ye will say to this mountain, Remove from here to there, and it will depart, and nothing will be impossible to you.
Yesu ya ce masu, “Saboda karancin bangaskiyarku. Domin hakika, ina gaya maku, in kuna da bangaskiya ko da kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan dutse, 'Matsa daga nan ka koma can,' zai kuwa matsa kuma ba abin da zai gagare ku.
21 But this kind does not go out except by prayer and fasting.
[Irin wannan aljanin bashi fita sai tare da addu'a da azumi].
22 And while they turned back in Galilee, Jesus said to them, The Son of man is going to be delivered into the hands of men,
Suna zaune a Galili, Yesu ya ce wa almajiransa, “Za a bada Dan Mutum ga hannun mutane.
23 and they will kill him, and the third day he will be raised up. And they were exceedingly sorry.
Kuma za su kashe shi, a rana ta uku zai tashi.” Sai almajiransa suka yi bakin ciki kwarai.
24 And when they came to Capernaum, those who receive the double-drachma came to Peter, and said, Does not your teacher pay the double-drachma?
Da suka iso Kafarnahum, mutane masu karbar haraji na rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku na ba da rabin shekel na haraji?”
25 He says, Yes. And when he entered into the house, Jesus anticipated him, saying, What think thou, Simon? The kings of the earth, from whom do they take taxes or tribute, from their sons or from strangers?
Sai ya ce, “I.” Amma da Bitrus ya shiga cikin gida, Yesu ya fara magana da shi yace, “Menene tunaninka Saminu? Sarakunan duniya, daga wurin wa suke karbar haraji ko kudin fito? Daga talakawansu ko daga wurin baki?”
26 And Peter says to him, From strangers. Jesus said to him, Therefore the sons are free.
Sai Bitrus ya ce, “Daga wurin baki,” Yesu ya ce masa, “Wato an dauke wa talakawansu biya kenan.
27 But, so that we might not offend them, after going to the sea, cast a hook. And take up the first fish coming up, and having opened its mouth, thou will find a four-drachma coin. After taking that, give thou to them for me and thee.
Amma don kada mu sa masu karbar harajin su yi zunubi, ka je teku, ka jefa kugiya, ka cire kifin da ya fara zuwa. Idan ka bude bakinsa, za ka sami shekel. Ka dauke shi ka ba masu karbar harajin nawa da naka.

< Matthew 17 >