< Mark 11 >

1 And when they came near to Jerusalem, to Bethphage and Bethany, at the mount of Olives, he sends forth two of his disciples,
Sa’ad da suka yi kusa da Urushalima, suka zo Betfaji da Betani wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki biyu daga cikin almajiransa,
2 and says to them, Go ye into the village opposite you, and straightaway as ye enter into it, ye will find a colt tied, on which none of men have ever sat. After untying it, bring it.
ya ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku, da shigarku, za ku tarar da wani ɗan jaki a daure a can, wanda ba wanda ya taɓa hawa. Ku kunce shi ku kawo nan.
3 And if any man should say to you, Why are ye doing this? say ye, The Lord has need of it, and straightaway he sends it here.
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke yin haka?’ Ku gaya masa cewa, ‘Ubangiji yana bukatarsa, zai kuma dawo da shi ba da jimawa ba.’”
4 And they departed, and found the colt tied by the door outside in the street, and they untied it.
Suka tafi, suka kuwa tarar da wani ɗan jaki a waje, a titi, daure a ƙofar gida. Suna cikin kunce shi ke nan,
5 And some of those who stood there said to them, What are ye doing, untying the colt?
sai waɗansu mutane da suke tsattsaye a wurin suka ce musu, “Me kuke yi da kuke kunce ɗan jakin nan?”
6 And they said to them just as Jesus commanded, and they allowed them.
Suka amsa kamar yadda Yesu ya ce su yi. Mutanen kuwa suka ƙyale su.
7 And they brought the colt to Jesus, and threw their garments on it, and he sat upon it.
Da suka kawo shi wajen Yesu, sai suka shimfiɗa rigunarsu a bayansa. Yesu kuwa ya hau ya zauna bisansa.
8 And many spread their garments upon the road, and others were cutting branches from the fields, and were spreading on the road.
Mutane da yawa suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya, waɗansu kuma suka baza rassan itatuwan da suka sara daga gonaki.
9 And those who went in front, and those who came behind, cried out saying, Hosanna! Blessed is he who comes in the name of the Lord!
Waɗanda suka yi gaba, da kuma waɗanda suke biye, duk suka ɗaga murya, suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa a cikin sunan Ubangiji!”
10 Blessed is the kingdom of our father David that comes in the name of the Lord! Hosanna in the highest!
“Mai albarka ne mulkin nan mai zuwa na mahaifinmu Dawuda!” “Hosanna a can cikin samaniya!”
11 And Jesus entered into Jerusalem, and into the temple. And when he looked around on all things, the hour now being evening, he went out to Bethany with the twelve.
Yesu ya shiga Urushalima ya kuma tafi filin haikali. Ya dudduba kome duka, amma da yake yamma ta yi, sai ya tafi Betani tare da Sha Biyun.
12 And on the morrow when they came out from Bethany he was hungry.
Kashegari, da suke barin Betani, Yesu kuwa ya ji yunwa.
13 And having seen a fig tree afar off having leaves, he came, if perhaps he will find anything on it. And when he came to it he found nothing except leaves, for it was not the time of figs.
Da ya hangi wani itacen ɓaure mai ganye, sai ya je domin yă ga ko yana da’ya’ya. Amma da ya kai can, bai tarar da kome ba sai ganye, domin ba lokacin’ya’yan ɓaure ba ne.
14 And having responded, Jesus said to it, No man may eat fruit from thee, no more into the age. And his disciples heard it. (aiōn g165)
Sai ya ce wa itacen, “Kada kowa yă ƙara cin’ya’yanka.” Almajiransa kuwa suka ji ya faɗi haka. (aiōn g165)
15 And they come to Jerusalem. And having entered into the temple, Jesus began to drive out those who sold and bought in the temple. And he overturned the tables of the moneychangers, and the seats of those who sold the doves.
Da suka kai Urushalima, sai Yesu ya shiga filin haikalin, ya fara korar waɗanda suke saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur na masu musayar kuɗi, da kujerun masu sayar da tattabaru,
16 And he did not permit that any man might carry a container through the temple.
ya kuma hana kowa yă ratsa da a filin haikali ɗauke da kayan ciniki.
17 And he taught, saying to them, Is it not written, My house will be called a house of prayer for all the nations? But ye made it a den of robbers.
Da yake koya musu, sai ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira gidana, gidan addu’a na dukan al’ummai ba’? Amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
18 And the scholars and the chief priests heard it, and sought how they might destroy him, for they feared him, because all the people were awed at his doctrine.
Manyan firistoci da malaman dokoki suka ji wannan, sai suka fara neman hanyar da za su kashe shi, gama suna jin tsoronsa, saboda dukan taron suna mamakin koyarwarsa.
19 And when it became evening he went forth outside of the city.
Da yamma ta yi, sai Yesu da almajiransa suka bar garin.
20 And passing by in the morning, they saw the fig tree dried out from the roots.
Da safe, da suke wucewa, sai suka ga itacen ɓauren nan ya yanƙwane tun daga saiwarsa.
21 And having remembered, Peter says to him, Rabbi, behold, the fig tree that thou cursed has been dried out.
Bitrus ya tuna, sai ya ce wa Yesu, “Rabbi, duba! Itacen ɓauren nan da ka la’anta, ya yanƙwane!”
22 And having answered, Jesus says to them, Have faith in God.
Yesu ya amsa ya ce, “Ku gaskata da Allah.
23 For truly I say to you, that whoever may say to this mountain, Be thou taken up and cast into the sea, and will not doubt in his heart, but will believe that what he says comes to pass, whatever he may say will be for him.
Gaskiya nake gaya muku, in wani ya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka fāɗa cikin teku,’ bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata cewa, abin da ya faɗa zai faru, haka kuwa za a yi masa.
24 Because of this I say to you, all things, as many as ye may ask, praying, believe that ye receive, and it will be for you.
Saboda haka, ina faɗa muku, duk abin da kuka roƙa cikin addu’a, ku gaskata kun riga kun karɓa, zai kuwa zama naku.
25 And whenever ye may stand praying, forgive, if ye have anything against any man, so that also your Father in the heavens will forgive you your trespasses.
A duk lokacin da kuke tsaye cikin addu’a, in kuna riƙe da wani mutum a zuciyarku, ku gafarta masa, domin Ubanku da yake sama shi ma yă gafarta muku zunubanku.”
26 But if ye do not forgive, neither will your Father in the heavens forgive your trespasses.
27 And they come again to Jerusalem. And as he was walking in the temple, the chief priests, and the scholars, and the elders come to him.
Suka sāke dawowa cikin Urushalima. Da Yesu yana tafiya a filin haikali, sai manyan firistoci, malaman dokoki da kuma dattawa suka zo wurinsa.
28 And they say to him, By what authority are thou doing these things? Or who gave thee this authority so that thou may do these things?
Suka tambaye, shi suka ce, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Wa kuma ya ba ka ikon yin wannan?”
29 And having answering, Jesus said to them, I also will question you one word, and answer me, and I will tell you by what authority I do these things.
Yesu ya ce, “Zan yi muku tambaya guda. Ku ba ni amsa, ni kuma zan gaya muku, ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
30 The immersion of John, was it from heaven, or from men? Answer me.
Baftismar Yohanna, daga sama ce, ko daga mutane? Ku faɗa mini!”
31 And they reasoned with themselves, saying, If we should say, From heaven, he will say, Why then did ye not believe him?
Sai suka tattauna a junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
32 But should we say, From men? (They feared the people, for all held John that he was indeed a prophet.)
In kuma muka ce, ‘Daga wurin mutane ne’; suna jin tsoron mutane, don kowa ya ɗauka cewa, Yohanna, annabi ne na gaskiya.”
33 And having answered, they say to Jesus, We do not know. And having answering, Jesus says to them, Neither do I tell you by what authority I do these things.
Saboda haka, suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”

< Mark 11 >