< Mark 10 >

1 And having risen from there, he comes into the borders of Judea through the other side of the Jordan. And multitudes come together to him again, and, as he has practiced, he taught them again.
Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
2 And the Pharisees having approached, they demanded of him if it is permitted for a man to divorce a wife, testing him.
Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
3 And having answered, he said to them, What did Moses command you?
Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 And they said, Moses permitted to write a document of divorce, and to divorce her.
Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
5 But having answered, Jesus said to them, For your hard heart he wrote for you this commandment.
Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
6 But from the beginning of creation God made them male and female.
Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
7 Because of this a man will leave his father and mother behind, and will be bonded with his wife,
‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
8 and the two will be in one flesh. So then they are no more two, but one flesh.
su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
9 What therefore God has joined together, no man shall separate.
Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
10 And in the house the disciples questioned him again about the same thing.
Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
11 And he says to them, Whoever may divorce his wife, and will marry another, commits adultery against her.
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
12 And if a woman should divorce her husband, and will be married to another, she commits adultery.
In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
13 And they brought children to him, so that he would touch them. And the disciples rebuked those who were bringing them.
Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
14 But when Jesus saw it, he was displeased, and said to them, Allow the children to come to me. Forbid them not, for of such is the kingdom of God.
Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
15 Truly I say to you, whoever will not receive the kingdom of God as a child, he will, no, not enter it.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
16 And having embraced them, while laying his hands upon them, he blessed them.
Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
17 And as he was going forth on the way, one man having ran to him, and having knelt to him, questioned him, Good teacher, what should I do that I may inherit eternal life? (aiōnios g166)
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
18 And Jesus said to him, Why do thou call me good? None is good except one, God.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
19 Thou know the commandments. Thou shall not commit adultery. Thou shall not murder. Thou shall not steal. Thou shall not testify falsely. Thou shall not defraud. Thou shall honor thy father and mother.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
20 And having answered, he said to him, Teacher, all these things I have observed from my youth.
Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
21 And having looked at him, Jesus loved him, and said to him, One thing thou lack. Go thou, sell as many things as thou have, and give to the poor, and thou will have treasure in heaven. And after taking up the cross, come, follow me.
Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
22 But having become somber at the saying, he went away sorrowing, for he was a man who has many possessions.
Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
23 And Jesus having looked around, he says to his disciples, How difficultly those who have riches will enter into the kingdom of God.
Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
24 And the disciples were astonished at his words. But again having answered, Jesus says to them, Children, how difficult it is for those who trust in riches to enter into the kingdom of God.
Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
25 It is easier for a camel to go through the hole of a needle, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
26 And they were exceedingly astonished, saying among themselves, Then who can be saved?
Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
27 And having looked at them, Jesus says, With men, impossible, but not with God. For with God all things are possible.
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
28 Peter began to say to him, Lo, we have left all, and have followed thee.
Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
29 And having answered, Jesus said, Truly I say to you, there is no man who has left house, or brothers, or sisters, or father, or mother, or wife, or children, or lands, because of me, and because of the good news,
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
30 but he will receive a hundredfold now in this time, houses, and brothers, and sisters, and mothers, and children, and lands-with persecutions-and in the coming age, eternal life. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 But many first will be last, and the last first.
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
32 And they were on the road going up to Jerusalem, and Jesus was going ahead of them. And they were amazed, and those who followed were afraid. And again having summoned the twelve, he began to tell them the things that were going to happen to him.
Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
33 Behold, we go up to Jerusalem. And the Son of man will be delivered to the chief priests and the scholars. And they will condemn him to death, and will deliver him to the Gentiles.
Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
34 And they will mock him, and will scourge, and will spit upon him, and will kill him. And the third day he will rise.
waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
35 And James and John, the sons of Zebedee, come to him, saying, Teacher, we wish that thou would do for us whatever we ask.
Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
36 And he said to them, What do ye want me to do for you?
Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
37 And they said to him, Grant to us that we may sit, one at thy right hand, and one at thy left hand, in thy glory.
Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
38 But Jesus said to them, Ye know not what ye are asking. Are ye able to drink the cup that I drink? And to be immersed the immersion that I am immersed?
Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
39 And they said to him, We are able. And Jesus said to them, Ye will indeed drink the cup that I drink, and the immersion that I am immersed ye will be immersed.
Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
40 But to sit at my right hand or at my left hand is not mine to give, but for whom it has been prepared.
amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
41 And when the ten heard it they began to indignant about James and John.
Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
42 And having summoned them, Jesus says to them, Ye know that those who presume to rule over the Gentiles, lord over them, and their great men have power over them.
Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
43 But it is not so among you. Instead, whoever may want to become great among you, will be your helper,
Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
44 and whoever of you may want to become first, will be a bondman of all.
Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
45 For the Son of man also came not to be served, but to serve, and to give his life a ransom for many.
Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
46 And they come to Jericho. And as he went out from Jericho, and his disciples and a considerable crowd, Bartimaeus, the blind son of Timaeus, was sitting by the road begging.
Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
47 And when he heard that it was Jesus the Nazarene, he began to cry out and say, Jesus, thou son of David, be merciful to me.
Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
48 And many rebuked him, that he would be quiet, but he cried out much more, Thou son of David, be merciful to me.
Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
49 And having stood still, Jesus said for him to be called. And they call the blind man, saying to him, Cheer up. Arise, he calls thee.
Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
50 And he, having thrown off his garment, having risen, came to Jesus.
Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
51 And having answered, Jesus says to him, What do thou want I would do to thee? And the blind man said to him, Rabboni, that I may receive my sight.
Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
52 And Jesus said to him, Go thou, thy faith has healed thee. And straightaway he received his sight, and followed him on the way.
Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.

< Mark 10 >