< Luke 19 >

1 And having entered, he was passing through Jericho.
Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
2 And behold, a man called by name, Zacchaeus. And he was a chief tax collector, and this man was rich.
Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
3 And he sought to see Jesus, who he was. And he was not able because of the crowd, because his stature was small.
Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
4 And having ran ahead, he climbed up in a sycamore tree so that he might see him, because he was going to pass that one.
Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
5 And when Jesus came to the place, having looked up, he saw him, and said to him, Zacchaeus, after making haste, come down, for today I must lodge at thy house.
Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
6 And having made haste, he came down and received him, rejoicing.
Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
7 And all who saw murmured, saying, He went in to relax with a sinful man.
Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
8 And having stood, Zacchaeus said to the Lord, Behold, half of the things possessed by me, Lord, I give to the poor. And if I defrauded any man of anything, I repay fourfold.
Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
9 And Jesus said to him, Today salvation has come to this house, forasmuch as he also is a son of Abraham.
Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
10 For the Son of man came to seek and to save that which was lost.
Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
11 And as they heard these things, he spoke, adding on a parable because he was near Jerusalem, and because they thought that the kingdom of God was going to appear immediately.
Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
12 He said therefore, A certain nobleman went into a far country to receive for himself a kingdom, and to return.
Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
13 And having called ten of his bondmen, he gave them ten minas and said to them, Do business until I come.
Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
14 But his citizens hated him, and sent an embassy behind him, saying, We do not want this man to reign over us.
“Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
15 And it came to pass for him to return, having taken the kingdom. And he said for these bondmen to be called to him, to whom he gave the silver, so that he might know what any man gained by trading.
“Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
16 And the first came, saying, Lord, thy mina gained ten minas.
“Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
17 And he said to him, Well, thou good bondman. Because thou became faithful in the least, be thou having authority over ten cities.
“Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
18 And the second came, saying, Lord, thy mina gained five minas.
“Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
19 And he also said to him, And thou become over five cities.
“Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
20 And another came, saying, Lord, behold thy mina, which I had put away in a napkin.
“Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
21 For I was afraid of thee because thou are an austere man. Thou take up what thou did not lay down, and reap what thou did not sow.
Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
22 He says to him, Out of thy mouth I will judge thee, thou evil bondman. Thou had known that I am an austere man taking up what I did not lay down, and reaping what I did not sow.
“Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
23 Then why did thou not give my silver into a bank, and having come I would have collected it with interest?
Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
24 And he said to those who stood by, Take the mina from him, and give it to him who has the ten minas.
“Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
25 And they said to him, Lord, he has ten minas.
“Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
26 For I say to you, that to every man who has, will be given, but from him who has not, even what he has will be taken away from him.
“Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
27 Nevertheless those enemies of mine who did not want me to reign over them, bring here, and kill them before me.
Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
28 And having spoke these things, he went ahead, going up to Jerusalem.
Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
29 And it came to pass when he came near to Bethphage and Bethany, at the mount that is called Olives, he sent two of his disciples, saying,
Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
30 Go ye into the opposite village, in which, having entered, ye will find a colt tied, on which no man ever sat. Having untied, bring it.
“Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
31 And if any man asks you, Why do ye untie it? Thus ye will say to him, The Lord has need of it.
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
32 And having departed, those who were sent found just as he said to them.
Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
33 And as they were untying the colt, the masters of it said to them, Why do ye untie the colt?
Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
34 And they said, The Lord has need of it.
Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
35 And they brought it to Jesus. And having cast their garments upon the colt, they mounted Jesus.
Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
36 And as he went, they spread their garments on the road.
Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
37 And as he was now coming near, at the descent of the mount of Olives, the whole multitude of the disciples began rejoicing to praise God in a great voice about all the mighty works that they had seen, saying,
Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
38 Blessed is the King who comes in the name of the Lord! Peace in heaven, and glory in the highest!
“Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
39 And some of the Pharisees from the multitude said to him, Teacher, rebuke thy disciples.
Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
40 And having answered, he said to them, I tell you that if these were silent, the stones would cry out.
Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
41 And when he came near, having seen the city, he wept over it,
Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
42 saying, If thou knew, even thou, indeed even in this thy day, the things for thy peace. But now they are hidden from thine eyes.
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
43 Because the days will come upon thee, and thine enemies will build a barricade around thee, and will surround thee, and enclose thee on every side.
Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
44 And they will raze thee and thy children within thee. And they will not leave in thee a stone upon a stone, because thou knew not the time of thy visitation.
Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
45 And having entered into the temple, he began to cast out those selling and buying in it,
Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
46 saying to them, It is written, My house is a house of prayer, but ye made it a den of robbers.
Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
47 And he was teaching daily in the temple. But the chief priests, and the scholars sought to destroy him, even the foremost men of the people.
Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
48 And they did not find what they might do, for the people all hung upon him, listening.
Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.

< Luke 19 >