< Joshua 6 >

1 Now Jericho was shut up tight because of the sons of Israel. None went out, and none came in.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 And Jehovah said to Joshua, See, I have given Jericho into thy hand, and the king of it, and the mighty men of valor.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 And ye shall encompass the city, all the men of war, going around the city once. Thus shall thou do six days.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 And seven priests shall bear seven trumpets of rams' horns before the ark. And the seventh day ye shall encompass the city seven times, and the priests shall blow the trumpets.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 And it shall be, that, when they make a long blast with the ram's horn, and when ye hear the sound of the trumpet, all the people shall shout with a great shout. And the wall of the city shall fall down flat, and the people shall go up every man straight before him.
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 And Joshua the son of Nun called the priests, and said to them, Take up the ark of the covenant, and let seven priests bear seven trumpets of rams' horns before the ark of Jehovah.
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 And they said to the people, Pass on, and encompass the city, and let the armed men pass on before the ark of Jehovah.
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 And it was so, that, when Joshua had spoken to the people, the seven priests bearing the seven trumpets of rams' horns before Jehovah passed on, and blew the trumpets. And the ark of the covenant of Jehovah followed them.
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 And the armed men went before the priests who blew the trumpets, and the rearward went behind the ark, the priests blowing the trumpets as they went.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 And Joshua commanded the people, saying, Ye shall not shout, nor let your voice be heard, neither shall any word proceed out of your mouth until the day I bid you shout. Then ye shall shout.
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 So he caused the ark of Jehovah to encompass the city, going around it once. And they came into the camp, and lodged in the camp.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 And Joshua rose early in the morning, and the priests took up the ark of Jehovah.
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 And the seven priests bearing the seven trumpets of rams' horns before the ark of Jehovah went on continually, and blew the trumpets. And the armed men went before them, and the rearward came behind the ark of Jehovah, the priests blowing the trumpets as they went.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 And the second day they encompassed the city once, and returned into the camp. So they did six days.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 And it came to pass on the seventh day, that they rose early at the dawning of the day, and encompassed the city according to the same manner seven times. Only on that day they encompassed the city seven times.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 And it came to pass at the seventh time, when the priests blew the trumpets, Joshua said to the people, Shout, for Jehovah has given you the city.
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 And the city shall be set apart, even it and all that is in it, to Jehovah. Only Rahab the harlot shall live, she and all who are with her in the house, because she hid the messengers that we sent.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 But as for you, only keep yourselves from what is set apart, lest when ye have set it apart, ye take from what is set apart. So ye would make the camp of Israel accursed, and trouble it.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 But all the silver, and gold, and vessels of brass and iron, are holy to Jehovah. They shall come into the treasury of Jehovah.
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 So the people shouted, and the priests blew the trumpets. And it came to pass, when the people heard the sound of the trumpet, that the people shouted with a great shout, and the wall fell down flat, so that the people went up into the city, every man straight before him, and they took the city.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 And they utterly destroyed all that was in the city, both man and woman, both young and old, and ox, and sheep, and donkey, with the edge of the sword.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 And Joshua said to the two men who had spied out the land, Go into the harlot's house, and bring out from there the woman, and all that she has, as ye swore to her.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 And the young men, the spies, went in, and brought out Rahab, and her father, and her mother, and her brothers, and all that she had. They also brought out all her kindred, and they set them outside the camp of Israel.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 And they burnt the city with fire, and all that was in it. Only the silver, and the gold, and the vessels of brass and of iron, they put into the treasury of the house of Jehovah.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 But Joshua saved alive Rahab the harlot, and her father's household, and all that she had. And she dwelt in the midst of Israel to this day, because she hid the messengers whom Joshua sent to spy out Jericho.
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 And Joshua charged them with an oath at that time, saying, Cursed be the man before Jehovah who rises up and builds this city Jericho. With the loss of his firstborn he shall lay the foundation of it, and with the loss of his youngest son he shall set up the gates of it.
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 So Jehovah was with Joshua, and his fame was in all the land.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.

< Joshua 6 >