< John 21 >

1 After these things Jesus manifested himself again to his disciples at the sea of Tiberias. And he revealed himself this way.
Bayan wadannan abubuwa, Yesu ya sake bayyana kansa ga almajiran a bakin tekun Tibariya. Ga yadda ya bayyana kansa:
2 There were together, Simon Peter, and Thomas called Didymus, and Nathanael of Cana in Galilee, and the sons of Zebedee, and two other men of his disciples.
Saminu Bitrus na tare da Toma wanda ake kira Dan Tagwai, da Natana'ilu daga Kana ta kasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma wadansu almajiran Yesu biyu.
3 Simon Peter says to them, I am going to harvest fish. They say to him, We also go with thee. They went forth, and straightaway entered into the boat. And in that night they caught nothing.
Saminu Bitrus yace masu, “Zani su.” sukace masa “Mu ma za mu je tare da kai.” Sai suka fita suka shiga jirgi, amma a daren nan basu kama komai ba.
4 But having now become morning, Jesus stood on the shore. However the disciples had not seen that it was Jesus.
To, gari na wayewa, sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran basu gane cewa Yesu bane.
5 Therefore Jesus says to them, Children, have ye anything eatable? They answered him, No.
Sai Yesu yace masu, “Samari, kuna da wani abinda za a ci?” Suka amsa masa sukace “A'a”.
6 And he said to them, Cast the net on the right side of the boat, and ye will find. Therefore they cast, and they were no longer able to draw it for the magnitude of fishes.
Yace masu, “Ku jefa taru dama da jirgin zaku samu wasu.” Suka jefa tarunsu har suka kasa jawo shi don yawan kifin.
7 That disciple therefore whom Jesus loved says to Peter, It is the Lord. So when Simon Peter heard that it is the Lord, he tied the coat around himself (for he was undressed), and threw himself into the sea.
Sai almajirin nan da Yesu yake kauna yace wa Bitrus, “Ubangiji ne fa!” Da Saminu Bitrus yaji, Ashe, Ubangiji ne, yayi damara da taguwarsa, (don a tube yake), ya fada a tekun.
8 And the other disciples came in the skiff (for they were not far from the land, but about two hundred cubits off), dragging the net of the fishes.
Sauran almajiran kuwa suka zo a cikin karamin jirgi, (domin basu da nisa da kasa, kamar kamu dari biyu zuwa sama), janye da tarun cike da kifi.
9 So when they came to the land, they saw a fire of coals set, and fish laying on it, and bread.
Da isowarsu gaci, sai suka ga garwashin wuta a wurin da kifi akai, da kuma gurasa.
10 Jesus says to them, Bring from the fishes that ye now caught.
Yesu ya ce masu “Ku kawo wandansu daga cikin kifin da kuka kama yanzu”.
11 Simon Peter went up, and drew the net to land, full of great fishes, a hundred and fifty-three. And being so many, the net was not broken.
Sai Saminu Bitrus ya hau, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu, tarun bai tsage ba.
12 Jesus says to them, Come, eat breakfast. And none of the disciples dared to query him, Who are thou? knowing that it is the Lord.
Yesu yace masu, “Ku zo ku karya kumallo”. Daga cikin almajiran kuwa babu wanda yayi karfin halin tambayarsa “Ko shi wanene?” Domin sunsani Ubangiji ne.
13 Jesus therefore comes, and takes the bread, and gives to them, and the fish likewise.
Yesu zo ya dauki gurasar ya ba su, haka kuma kifin.
14 This is now a third time Jesus was manifested to his disciples after being raised from the dead.
Wannan shine karo na uku da Yesu ya bayyana ga almajiransa bayan tashinsa daga matattu.
15 So when they ate breakfast, Jesus says to Simon Peter, Simon, son of Jonah, do thou love me more than these things? He says to him, Yea, Lord. Thou know that I love thee. He says to him, Feed my lambs.
Da suka karya kumallon, Yesu yace wa Saminu Bitrus, “Bitrus dan Yahaya, kana kaunata fiye da wadannan?” Bitrus yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka” Yesu yace masa “Ka ciyar da 'ya'yan tumakina”.
16 He says to him again a second time, Simon, son of Jonah, do thou love me? He says to him, Yea, Lord. Thou know that I love thee. He says to him, Feed my sheep.
Ya sake fada masa karo na biyu, “Saminu Dan Yahaya, kana kaunata?” Bitrus Yace masa “I ya Ubangiji, ka sani ina kaunarka”. Yesu yace masa, “Ka lura da Tumakina”.
17 He says to him the third time, Simon, son of Jonah, do thou love me? Peter was grieved because he said to him the third time, Do thou love me? And he said to him, Lord, thou know all things. Thou know that I love thee. Jesus says to him, Feed my sheep.
Ya sake fada masa, karo na uku, “Bitrus Dan Yahaya, kana kaunata? Sai Bitrus bai ji dadi ba domin Yesu ya fada masa karo na uku, “Kana kaunata” Yace masa, “Ubangiji ka san komai duka, ka sani ina kaunarka.” Yesu yace masa “Ka ciyar da tumaki na.
18 Truly, truly, I say to thee, When thou were younger, thou girded thyself, and walked where thou would, but when thou become old, thou will stretch forth thy hands, and another will gird thee, and carry thee where thou do not want.
Hakika, hakika, Ina gaya maka, lokacin da kake kuruciyarka, kakan yi wa kanka damara, ka tafi inda ka ga dama. amma in ka tsufa, zaka mike hannuwanka wani yayi maka damara, ya kai ka inda baka nufa ba.”
19 Now he said this, signifying by what kind of death he will glorify God. And after saying this, he says to him, Follow me.
To Yesu ya fadi haka ne domin ya nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi ga daukakar Allah. Bayan ya fadi haka, sai yace wa Bitrus, ka biyo ni.
20 But Peter, having turned around, sees the disciple whom Jesus loves, following, who also leaned near his chest at the supper, and said, Lord, who is the man betraying thee?
Bitrus ya juya sai ya ga almajirin da Yesu yake kauna yana biye dasu; wanda ya jingina a kirgin Yesu lokacin cin jibin nan da yace “Ya Ubangiji, wanene zai bashe ka?”
21 Having seen this man, Peter says to Jesus, Lord, and what of this man?
Da Bitrus ya gan shi, yace wa Yesu “Ya Ubangiji, Me mutumin nan zai yi?”
22 Jesus says to him, If I want him to remain until I come, what is it to thee? Follow thou me.
Yesu yace masa, “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka? Ka biyo ni.”
23 This saying therefore went forth among the brothers, that that disciple does not die. And yet Jesus did not say to him, that he does not die, but, If I want him to remain until I come, what is it to thee?
Wannan zance ya yadu cikin 'yan'uwa cewa, wannan almajirin ba zai mutu ba. Alhali Yesu bai cewa Bitrus, wannan almajirin ba zai mutu ba, Amma “Idan ina so ya zauna har in dawo ina ruwanka?”
24 This is the disciple who testifies about these things, and who wrote these things. And we know that his testimony is true.
Wannan shine almajirin da yake shaida wadannan abubuwa, wanda ya rubuta su, kuma mun tabbata shaidarsa gaskiya ne.
25 And there are also many other things, as many as Jesus did, which if they would be written every one, I suppose not even the world itself to make room for the books being written. Truly.
Akwai kuma sauran abubuwa da yawa wanda Yesu yayi. Idan da an rubuta kowannensu daya bayan daya, ina gaya maku, ko duniya bazata iya daukar litattafan da za a rubuta ba.

< John 21 >