< Job 12 >
1 Then Job answered and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 No doubt but ye are the people, and wisdom shall die with you.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 But I have understanding as well as you; I am not inferior to you. Yes, who does not know such things as these?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 I am as a man who is a laughing-stock to his neighbor. I who called upon God, and he answered. The just, the perfect man is a laughing-stock.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 In the thought of him who is at ease there is contempt for calamity. It is ready for those whose foot slips.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 The tents of robbers prosper, and those who provoke God are secure. Into whose hand God brings abundantly.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 But ask now the beasts, and they shall teach thee, and the birds of the heavens, and they shall tell thee.
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Or speak to the earth, and it shall teach thee, and the fishes of the sea shall declare to thee.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Who does not know in all these, that the hand of Jehovah has wrought this,
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 in whose hand is the soul of every living thing, and the breath of all mankind?
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Does not the ear try words, even as the palate tastes its food?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 With aged men is wisdom, and in length of days understanding.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 With God is wisdom and might. He has counsel and understanding.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Behold, he breaks down, and it cannot be built again. He shuts up a man, and there can be no opening.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Behold, he withholds the waters, and they dry up. Again, he sends them out, and they overturn the earth.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 With him is strength and wisdom. The deceived and the deceiver are his.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 He leads counselors away stripped, and he makes judges fools.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 He loosens the bond of kings, and he binds their loins with a belt.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 He leads priests away stripped, and overthrows the mighty.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 He removes the speech of the trustworthy, and takes away the understanding of the elders.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 He pours contempt upon rulers, and weakens the strength of the strong.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 He uncovers deep things out of darkness, and brings out to light the shadow of death.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 He increases the nations, and he destroys them. He enlarges the nations, and he leads them captive.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 He takes away understanding from the chiefs of the people of the earth, and causes them to wander in a wilderness where there is no way.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 They grope in the dark without light, and he makes them to stagger like a drunken man.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.