< Jeremiah 13 >

1 Thus says Jehovah to me, Go, and buy thee a linen sash, and put it upon thy loins, and do not put it in water.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2 So I bought a sash according to the word of Jehovah, and put it upon my loins.
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3 And the word of Jehovah came to me the second time, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4 Take the sash that thou have bought, which is upon thy loins, and arise, go to the Euphrates, and hide it there in a cleft of the rock.
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5 So I went, and hid it by the Euphrates, as Jehovah commanded me.
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
6 And it came to pass after many days, that Jehovah said to me, Arise, go to the Euphrates, and take the sash from there, which I commanded thee to hide there.
Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
7 Then I went to the Euphrates, and dug, and took the sash from the place where I had hid it. And, behold, the sash was rotten. It was good for nothing.
Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
8 Then the word of Jehovah came to me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Thus says Jehovah, After this manner I will mar the pride of Judah, and the great pride of Jerusalem.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
10 This evil people, who refuse to hear my words, who walk in the stubbornness of their heart, and have gone after other gods to serve them, and to worship them, shall even be as this sash, which is good for nothing.
Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
11 For as the sash clings to the loins of a man, so I have caused to cling to me the whole house of Israel and the whole house of Judah, says Jehovah, that they may be to me for a people, and for a name, and for a praise, and for a glory, but they would not hear.
Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
12 Therefore thou shall speak to them this word. Thus says Jehovah, the God of Israel: Every bottle shall be filled with wine. And they shall say to thee, Do we not certainly know that every bottle shall be filled with wine?
“Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
13 Then thou shall say to them, Thus says Jehovah: Behold, I will fill all the inhabitants of this land, even the kings who sit upon David's throne, and the priests, and the prophets, and all the inhabitants of Jerusalem, with drunkenness.
Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
14 And I will dash them one against another, even the fathers and the sons together, says Jehovah. I will not pity, nor spare, nor have compassion, that I should not destroy them.
Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
15 Hear ye, and give ear, be not proud, for Jehovah has spoken.
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16 Give glory to Jehovah your God, before he causes darkness, and before your feet stumble upon the dark mountains. And, while ye look for light, he turns it into the shadow of death, and makes it gross darkness.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
17 But if ye will not hear it, my soul shall weep in secret for your pride. And my eye shall weep greatly, and run down with tears, because Jehovah's flock is taken captive.
Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
18 Say thou to the king and to the queen-mother: Humble yourselves. Sit down, for your coronets have come down, even the crown of your glory.
Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
19 The cities of the South are shut up, and there is none to open them. Judah is carried away captive, all of it. It is wholly carried away captive.
Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
20 Lift up your eyes, and behold those who come from the north. Where is the flock that was given thee, thy beautiful flock?
Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
21 What will thou say when he shall set over thee as head those whom thou thyself have taught to be friends to thee? Shall not sorrows take hold of thee as of a woman in travail?
Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
22 And if thou say in thy heart, Why have these things come upon me? For the greatness of thine iniquity thy skirts are uncovered, and thy heels suffer violence.
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23 Can the Ethiopian change his skin, or the leopard his spots? Then ye also may do good, who are accustomed to do evil.
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24 Therefore I will scatter them as the stubble that passes away by the wind of the wilderness.
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25 This is thy lot, the portion measured to thee from me, says Jehovah, because thou have forgotten me, and trusted in falsehood.
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26 Therefore I will also uncover thy skirts upon thy face, and thy shame shall appear.
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27 I have seen thine abominations, even thine adulteries, and thy neighings, the lewdness of thy whoredom, on the hills, in the field. Woe to thee, O Jerusalem! Thou will not be made clean. How long shall it yet be?
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”

< Jeremiah 13 >