< Isaiah 33 >

1 Woe to thee who destroys, and thou were not destroyed, and deal treacherously, and they did not deal treacherously with thee! When thou have ceased to destroy, thou shall be destroyed, and when thou have made an end of dealing treacherously, they shall deal treacherously with thee.
Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
2 O Jehovah, be gracious to us, we have waited for thee. Be thou our arm every morning, also our salvation in the time of trouble.
Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
3 At the noise of the tumult the peoples have fled. At the lifting up of thyself the nations are scattered.
Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
4 And your spoil shall be gathered as the caterpillar gathers. As locusts leap, men shall leap upon it.
Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
5 Jehovah is exalted, for he dwells on high. He has filled Zion with justice and righteousness.
Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
6 And there shall be stability in thy times, abundance of salvation, wisdom, and knowledge. The fear of Jehovah is thy treasure.
Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
7 Behold, their valiant ones cry outside. The ambassadors of peace weep bitterly.
Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
8 The highways lie waste. The wayfaring man ceases. The enemy has broken the covenant. He has despised the cities. He does not regard man.
An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
9 The land mourns and languishes. Lebanon is confounded and withers away. Sharon is like a desert, and Bashan and Carmel shake off their leaves.
Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
10 Now I will arise, says Jehovah. Now I will lift up myself. Now I will be exalted.
“Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
11 Ye shall conceive chaff. Ye shall bring forth stubble. Your breath is a fire that shall devour you.
Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
12 And the peoples shall be as the burnings of lime, as thorns cut down that are burned in the fire.
Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
13 Hear, ye who are far off, what I have done, and ye who are near, acknowledge my might.
Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
14 The sinners in Zion are afraid. Trembling has seized the profane. Who among us can dwell with the devouring fire? Who among us can dwell with everlasting burnings?
Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
15 He who walks righteously, and speaks uprightly. He who despises the gain of oppressions, who shakes away his hands from taking a bribe, who stops his ears from hearing of blood, and shuts his eyes from looking upon evil.
Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
16 He shall dwell on high. His place of defense shall be the munitions of rocks. His bread shall be given. His waters shall be sure.
shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
17 Thine eyes shall see the king in his beauty. They shall behold a land that reaches afar.
Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
18 Thy heart shall muse on the terror. Where is he who counted? Where is he who weighed the tribute? Where is he who counted the towers?
Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
19 Thou shall not see the fierce people, a people of a deep speech that thou cannot comprehend, of a strange tongue that thou cannot understand.
Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
20 Look upon Zion, the city of our solemnities. Thine eyes shall see Jerusalem a quiet habitation, a tent that shall not be removed. The stakes of which shall never be plucked up, nor shall any of the cords of it be broken.
Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
21 But Jehovah will be with us there in majesty. A place of broad rivers and streams, in which shall go no galley with oars, nor shall a gallant ship pass thereby.
A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
22 For Jehovah is our judge. Jehovah is our lawgiver. Jehovah is our king, he will save us.
Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
23 Thy tacklings are loosed. They could not strengthen the foot of their mast. They could not spread the sail. Then the prey of a great spoil was divided. The lame took the prey.
Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
24 And the inhabitant shall not say, I am sick. The people who dwell in it shall be forgiven their iniquity.
Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.

< Isaiah 33 >