< Hebrews 12 >

1 Therefore we also, having so great a cloud of witnesses surrounding us, having put off every weight and cleverly entangling sin, let us run by perseverance the contest being set before us.
Da shike muna kewaye da wannan irin kasaitaccen taro na shaidu, sai mu watsar da dukkan abubuwan dake nawaita mana da kuma zunubin da zai saurin makale ma na. Bari a cikin hakuri mu yi tseren da ke gabanmu.
2 Looking to Jesus the pathfinder and perfecter of the faith, who, against the joy set before him, endured a cross, having despised the shame, and has sat down at the right hand of the throne of God.
Bari mu kafa idonmu ga Yesu, wanda shine mafarin bangaskiyarmu da cikarta. Wanda sabili da murnar da a ka sa a gabansa ya jimre giciye, ya kuma yi watsi da kunyarsa, wanda kuma ya zauna a hannun dama na kursiyin Allah.
3 For consider the man who endured such hostility against him by sinners, so that ye may not be weary in your souls, being disheartened.
Ku dube shi wanda ya jimre irin wannan adawa daga masu zunubi, domin kada ku gaji ko ku karai.
4 Ye have not yet resisted as far as blood, struggling against sin.
Ba ku yi tsayayya ko jayayya da zunubi har ta kai ga zub da jininku ba tukunna. Kun kuma manta da gargadin da a ka yi maku a matsayin 'ya'ya:
5 And have ye forgotten the exhortation that reasons with you as with sons, My son, do not disparage the chastening of the Lord, nor become disheartened when punished by him?
''Dana, kada ka dauki horon Ubangiji da wasa, kadda kuma ka yi suwu lokacin da ka sami horonsa,''
6 For whom the Lord loves he chastens. And he whips every son whom he receives.
Domin kuwa Ubangiji yana horon dukkan wadanda yake kauna, yana kuma hukunta duk wadanda ya karba.
7 Because of chastening ye endure; God is treating you as with sons, for what son is there whom a father does not chasten?
Ku daure wahala a matsayin horo. Allah yana yi da ku kamar 'ya'yansa, domin kuwa wanne da ne wanda ubansa bazai yi masa horo ba?
8 And if ye are without chastening, of which all have become participants, then ye are bastards, and not sons.
Amma idan baku da horo kamar yadda sauran mutane ke da shi, kun zama shegu kenan ba 'ya'ya ba.
9 Besides, we indeed have had chastisers-the fathers of our flesh-and we were turned around. Shall we not much more be subordinate to the Father of the spirits, and we will live?
Hakannan kuma kamar yadda muke da iyaye a duniya wadanda suke yi mana horo, kuma muna basu daraja. To ba sai mu yiwa Ubanmu na Ruhaniya biyayya don mu rayu ba?
10 For those men indeed for a few days chastened us according to that which seemed good to them, but he for that which is advantageous, in order to be partakers of his holiness.
Ta wani fanni kuwa iyayenmu suna yi mana horo na kwanaki kadan bisa ga yadda suka ga ya dace, Amma Allah kuwa yana yi mana horo domin anfanin kanmu, domin kuma mu sami rabo daga cikin tsarkinsa.
11 But of course no chastening for the present seems to be of joy but of sorrow, yet afterward it yields peaceable fruit of righteousness to those who have been trained by it.
Ba horon da ke da dadi a lokacin yinsa, amma sai zafi. Sai dai kuma bayan haka yakan haifar da 'ya'ya na ruhaniya da kuma adalci ga dukkan wadanda aka yi rainonsu a ciki.
12 Therefore lift up the drooping hands, and the feeble knees,
Don haka sai ku karfafa hannayenku da ke reto, da kuma guwawunku da ke kaduwa.
13 and make straight paths for your feet, so that what is lame may not be turned away, but may be healed instead.
Ku bi hanyoyi mikakku domin abin da ya gurgunce kada ya karye amma ya warke.
14 Pursue peace with all men, and the sanctification without which no man will see the Lord.
Ku bidi salama da kowa, da kuma rayuwar tsarki wanda in ba tare da shi, babu wanda zai ga Allah.
15 Looking carefully lest any man fall short, away from the grace of God, lest any root of bitterness sprouting up would cause trouble, and by this many may be defiled,
Ku mai da hankali domin kada waninku ya rasa, alherin Allah, kuma kada wani tushe mai daci ya tsiro a cikinku har ya haifar da fitina, domin kada da dama daga cikinku su gurbata ta wurinsa.
16 lest a fornicator or profane man like Esau, who, in place of one meal sold his birthright.
Ku yi hankali kuma kada a sami mazinanci ko marar ibada a cikinku, kamar Isuwa, wanda sabili da abinci ya sayar da 'yancinsa na dan fari.
17 For ye also know that wanting afterward to inherit the blessing, he was rejected, for he found no place of repentance, though having sought it with tears.
Kun kuwa san cewa sa'adda ya yi marmarin ya gaji albarka a gaba, an kishi, domin kuwa bai sami damar tuba ba, ko da shike ya nema har da hawaye.
18 For ye have not come to a mountain being felt, and which burned with fire, and to darkness, and gloom, and a tempest,
Domin kuwa baku zo ga dusen da ake tabawa da hannu ba, dutse ne mai ci da wuta, da tukuki da bakin hayaki da hadari.
19 and a sound of a trumpet, and a voice of words, of which those who heard begged that a word not be added to them.
Ba Ku zo ga karar kaho mai ban razana da murya mai firgitarwa ba, da masu sauraro suka yi roko kar su sake jinta.
20 For they did not bear that which was commanded, if even a beast should touch the mountain, it shall be stoned.
Don basu iya jimre abin da aka yi doka a kan saba: ''koma dabba ce ta taba dutsen, sai a jejjefe ta.''
21 And so fearful was that which was made visible, that Moses said, I am terrified and trembling.
Abin tsoro ne kuwa kwarai, har Musa yace, ''A tsoroce nake kwarai har na firgita.''
22 But ye have come to mount Zion, and to the city of a living God, a heavenly Jerusalem, and to myriads of agents,
Maimakon haka kun zone ga Dutsen Sihiyona da kuma birni na Allah mai Rai, kuma na Urushalima ta Samniya, da kuma dubun dubban mala'iku cikin murna da farin ciki.
23 to a festal gathering and assembly of firstborn sons who were enrolled in the heavens, and to God, a Judge of all, and to spirits of righteous men who were made fully perfect,
Kun zo taro na dukkan 'ya'yan fari, rubuttatu a sama, kuma kun zo ga Allah wanda shine alkalin dukka, hakannan kuma zuwa ga ruhu na adalai wanda a ka rigaya aka tsarkake.
24 and to Jesus a mediator of a new covenant, and to blood of sprinkling that speaks better than Abel.
Kun zo ga Yesu, wanda shine matsakancin sabon alkawari, kuma ga jinin yayyafawa da ke magana fiye da na jinin Habila.
25 Watch, that ye not refuse him who speaks. For if those men did not escape, having refused him who spoke a divine message on earth, much more we, those who turn away from him from the heavens,
Ku yi lura kada ku ki wannan da ke yi mu ku magana. Gama in har basu kubuta yayin da su ka yi jayayya da wanda ya yi mu su gargadi a duniya ba, balle ma mu ba za mu kubuta ba in mun ki wanda ke mana gargadi daga sama.
26 whose voice then shook the earth. But now he has promised, saying, Yet once, I shake not only the earth, but also the heaven.
A wani karo, muryar sa ta girgiza duniya. Amma yanzu yayi alkawari da cewa, ''Har'ila yau ba duniyar kadai zan girgiza ba, amma har da sammai.''
27 And the, Yet once, signifies the removal of the things being shaken-as of things that were made-so that the things not being shaken may remain.
Wannan kalma, ''Harl'ila yau,'' ta bayyana cirewar abubuwan nan da za su girgizu, wato abubuwan da a ka halitta, domin abubuwan da ba zasu girgizu ba su kasance.
28 Therefore, receiving an immovable kingdom, we may have grace, through which we may serve God acceptably with reverence and awe.
Don haka, samun mulkin da ba za ya girgizu ba, sai mu zama masu godiya, kuma a cikin wannan yanayi mu yi wa Allah sujada cikin daraja da tsaninin gimamawa.
29 For our God is also a consuming fire.
Domin kuwa Allahnmu wuta ne mai konewa.

< Hebrews 12 >