< Hebrews 11 >
1 Now faith is the foundation of hoping, the evidence of events not being seen.
Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
2 For by this the ancients were well reported.
Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
3 By faith we understand the ages to have been prepared by the word of God. For the things that are seen do not come to be from that which is visible. (aiōn )
Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn )
4 By faith Abel offered to God a better sacrifice than Cain, because of which he was reported to be righteous, God testifying about his gifts, and through it, he who died still speaks.
Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
5 By faith Enoch was transferred to not see death, and he was not found, because God transferred him. For before his removal he was reported to be pleasing to God.
Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
6 And apart from faith it is impossible to please him. For he who comes to God must believe that he is, and becomes a rewarder of those who search for him.
In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
7 By faith Noah, being divinely warned about things not yet seen, moved with awe, prepared an ark for the salvation of his house, through which he condemned the world, and became an heir of righteousness according to faith.
Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
8 By faith Abraham, when called, obeyed to go out to the place that he was going to take for an inheritance. And he went out, not knowing where he was going.
Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
9 By faith he lived alien in the land of promise as a foreigner, having dwelt in tents with Isaac and Jacob, the fellow heirs of the same promise.
Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
10 For he anticipated the city that has the foundations, whose builder and architect is God.
Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
11 By faith even Sarah herself received power for conception of seed, and she gave birth beyond the time of age, because she considered him faithful who promised.
Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
12 And therefore from one man, and these things having become deadened, were begotten as the stars of the heaven for multitude, and as the sand of the seashore, countless.
Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
13 All these died in faith, not having taken the promises, but who saw and greeted them from afar, and who confessed that they were foreigners and sojourners on the earth.
Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
14 For those who say such things show that they are seeking a fatherland.
Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
15 And if indeed they remembered that from which they came out, they would have had time to return.
Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
16 But now they aspire for a superior one, that is, a heavenly one. Therefore God is not ashamed of them, to be called their God, for he has prepared for them a city.
A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
17 By faith Abraham, being tested, offered Isaac. And he who received the promises offered his only begotten son,
Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
18 about whom it was said, The seed by thee will be called in Isaac.
ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
19 Having reckoned that God is able to raise up even from the dead, from where also, in a figure, he did receive him back.
Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
20 By faith Isaac blessed Jacob and Esau about things coming.
Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
21 By faith Jacob, while dying, blessed each of the sons of Joseph, and bowed in worship upon the top of his staff.
Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
22 By faith Joseph, while perishing, remembered about the exodus of the sons of Israel, and commanded about his bones.
Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
23 By faith Moses, after being born, was hid three months by his parents, because they saw the child well-formed, and they were not afraid of the king's edict.
Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
24 By faith Moses, having become great, refused to be called the son of Pharaoh's daughter,
Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
25 having chosen rather to be mistreated with the people of God, than to have the pleasure of sin temporarily.
Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
26 Having esteemed the vilification of the Christ greater wealth than the treasures of Egypt, for he focused toward the recompense of reward.
Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
27 By faith he forsook Egypt, not having feared the wrath of the king, for he persevered as seeing the invisible.
Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
28 By faith he performed the Passover and the sprinkling of the blood, so that he who was destroying the firstborn would not touch them.
Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
29 By faith they passed through the Red sea as by dry land, of which the Egyptians, having taken an attempt, were drowned.
Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
30 By faith the walls of Jericho fell down, having been encircled for seven days.
Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
31 By faith Rahab the harlot was not destroyed with those who were disobedient, having received the spies with peace.
Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
32 And what shall I say further? For the time would fail me telling about Gideon, also Barak and Samson and Jephthah, also of David and Samuel and the prophets,
Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
33 who, through faith, conquered kingdoms, wrought righteousness, obtained promises, closed the mouths of lions,
waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
34 quenched the force of fire, escaped the jaw of the sword. Out of weakness were made strong, became mighty in war, bowed down armies of aliens.
suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
35 Women took hold of their dead from a resurrection, but others were tortured, not having accepted deliverance, so that they might experience a superior resurrection.
Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
36 And others took a trial of mockings and scourgings, and moreover of bonds and imprisonment.
Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
37 They were stoned, they were sawed apart, they were tempted, they died in murder by sword. They wandered about in sheepskins, in goatskins, being destitute, restricted, tormented
Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
38 (of whom the world was not worthy), wandering in deserts and mountains and caves, and the holes of the earth.
duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
39 And all these, having been well reported through faith, did not receive the promise,
Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
40 God having foreseen something superior concerning us, so that without us they would not be made fully perfect.
Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.