< Ezekiel 24 >
1 Again, in the ninth year, in the tenth month, in the tenth day of the month, the word of Jehovah came to me, saying,
A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, write thee the name of the day, even of this selfsame day; the king of Babylon drew close to Jerusalem this selfsame day.
“Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
3 And utter a parable to the rebellious house, and say to them, Thus says the lord Jehovah: Set on the caldron. Set it on, and also pour water into it.
Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
4 Gather the pieces of it into it, even every good piece, the thigh, and the shoulder; fill it with the choice bones.
Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
5 Take the choice of the flock, and also a pile of wood for the bones under the caldron. Make it boil well, yea, let the bones of it be boiled in the midst of it.
ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
6 Therefore thus says the lord Jehovah: Woe to the bloody city, to the caldron whose rust is therein, and whose rust has not gone out of it! Take out of it piece after piece. No lot has fallen upon it.
“‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
7 For her blood is in the midst of her. She set it upon the bare rock. She did not pour it upon the ground to cover it with dust.
“‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
8 That it may cause wrath to come up to take vengeance, I have set her blood upon the bare rock, that it should not be covered.
Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
9 Therefore thus says the lord Jehovah: Woe to the bloody city! I also will make the pile great.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
10 Heap on the wood; make the fire hot. Boil the flesh well, and make the broth thick. And let the bones be burned.
Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
11 Then set it empty upon the coals of it, that it may be hot, and the brass of it may burn, and that the filthiness of it may be molten in it, that the scum of it may be consumed.
Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
12 She has wearied herself with toil, yet her great scum does not go forth out of her, her scum by fire.
Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
13 In thy filthiness is lewdness. Because I have cleansed thee and thou were not cleansed, thou shall not be cleansed from thy filthiness any more, till I have caused my wrath toward thee to rest.
“‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
14 I, Jehovah, have spoken it. It shall come to pass, and I will do it. I will not go back. I will neither spare, nor will I relent. According to thy ways, and according to thy doings, they shall judge thee, says the lord Jehovah.
“‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 Also the word of Jehovah came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Son of man, behold, I take the desire of thine eyes away from thee with a stroke. Yet thou shall neither mourn nor weep. Neither shall thy tears run down.
“Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
17 Sigh, but not aloud. Make no mourning for the dead. Bind thy headdress upon thee, and put thy shoes upon thy feet. And do not cover thy lips, and do not eat the bread of men.
Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
18 So I spoke to the people in the morning, and at evening my wife died. And I did in the morning as I was commanded.
Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
19 And the people said to me, Will thou not tell us what these things are to us, that thou do so?
Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
20 Then I said to them, The word of Jehovah came to me, saying,
Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
21 Speak to the house of Israel, Thus says the lord Jehovah: Behold, I will profane my sanctuary, the pride of your power, the desire of your eyes, and that which your soul has compassion. And your sons and your daughters whom ye have left behind shall fall by the sword.
faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
22 And ye shall do as I have done. Ye shall not cover your lips, nor eat the bread of men.
Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
23 And your coverings shall be upon your heads, and your shoes upon your feet. Ye shall not mourn nor weep, but ye shall pine away in your iniquities, and moan one toward another.
Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
24 Thus Ezekiel shall be to you a sign, according to all that he has done ye shall do. When this comes, then ye shall know that I am the lord Jehovah.
Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
25 And thou, son of man, shall it not be in the day when I take from them their strength, the joy of their glory, the desire of their eyes, and that upon which they set their heart-their sons and their daughters-
“Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
26 that in that day he who escapes shall come to thee, to cause thee to hear it with thine ears?
a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
27 In that day thy mouth shall be opened to him who is escaped, and thou shall speak, and no more be mute. So thou shall be a sign to them, and they shall know that I am Jehovah.
A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”