< Deuteronomy 3 >

1 Then we turned, and went up the way to Bashan. And Og the king of Bashan came out against us, he and all his people, to battle at Edrei.
Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
2 And Jehovah said to me, Fear him not, for I have delivered him, and all his people, and his land, into thy hand. And thou shall do to him as thou did to Sihon king of the Amorites, who dwelt at Heshbon.
Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
3 So Jehovah our God delivered into our hand Og also, the king of Bashan, and all his people, and we smote him until none was left to him remaining.
Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
4 And we took all his cities at that time. There was not a city which we did not take from them, sixty cities, all the region of Argob, the kingdom of Og in Bashan.
A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
5 All these were cities fortified with high walls, gates, and bars; besides the un-walled towns a great many.
Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
6 And we utterly destroyed them, as we did to Sihon king of Heshbon, utterly destroying every inhabited city, with the women and the little ones.
Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
7 But all the cattle, and the spoil of the cities, we took for a prey to ourselves.
Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
8 And we took the land at that time out of the hand of the two kings of the Amorites who were beyond the Jordan, from the valley of the Arnon to mount Hermon
A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
9 (the Sidonians call Hermon, Sirion, and the Amorites call it Senir),
(Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
10 all the cities of the plain, and all Gilead, and all Bashan, to Salecah and Edrei, cities of the kingdom of Og in Bashan.
Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
11 (For only Og king of Bashan remained of the remnant of the Rephaim. Behold, his bedstead was a bedstead of iron. Is it not in Rabbah of the sons of Ammon? Nine cubits was the length of it, and four cubits the breadth of it, after the cubit of a man.)
(Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
12 And we took this land in possession at that time. From Aroer, which is by the valley of the Arnon, and half the hill-country of Gilead, and the cities of it, I gave to the Reubenites and to the Gadites.
Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
13 And the rest of Gilead, and all Bashan, the kingdom of Og, I gave to the half-tribe of Manasseh, all the region of Argob, even all Bashan. The same is called the land of Rephaim.
Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
14 (Jair the son of Manasseh took all the region of Argob, to the border of the Geshurites and the Maacathites, and called them, even Bashan, after his own name, Havvoth-jair, to this day.)
Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
15 And I gave Gilead to Machir.
Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
16 And I gave to the Reubenites and to the Gadites from Gilead even to the valley of the Arnon, the middle of the valley, and the border of it, even to the river Jabbok, which is the border of the sons of Ammon,
Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
17 also the Arabah, and the Jordan and the border of it, from Chinnereth even to the sea of the Arabah, the Salt Sea, under the slopes of Pisgah eastward.
Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
18 And I commanded you at that time, saying, Jehovah your God has given you this land to possess it. Ye shall pass over armed before your brothers the sons of Israel, all the men of valor.
Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
19 But your wives, and your little ones, and your cattle, (I know that ye have much cattle, ) shall abide in your cities which I have given you
Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
20 until Jehovah gives rest to your brothers, as to you, and they also possess the land which Jehovah your God gives them beyond the Jordan, then ye shall return every man to his possession, which I have given you.
sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
21 And I commanded Joshua at that time, saying, Thine eyes have seen all that Jehovah your God has done to these two kings. So shall Jehovah do to all the kingdoms where thou go over.
A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
22 Ye shall not fear them, for Jehovah your God, he it is who fights for you.
Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
23 And I besought Jehovah at that time, saying,
A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
24 O lord Jehovah, thou have begun to show thy servant thy greatness, and thy strong hand, for what god is there in heaven or in earth, that can do according to thy works, and according to thy mighty acts?
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
25 Let me go over, I pray thee, and see the good land that is beyond the Jordan, that goodly mountain, and Lebanon.
Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
26 But Jehovah was angry with me because of you, and did not hearken to me. And Jehovah said to me, It shall be enough for thee. Speak no more to me of this matter.
Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
27 Get thee up to the top of Pisgah, and lift up thine eyes westward, and northward, and southward, and eastward, and behold with thine eyes, for thou shall not go over this Jordan.
Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
28 But charge Joshua, and encourage him, and strengthen him, for he shall go over before this people, and he shall cause them to inherit the land which thou shall see.
Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
29 So we abode in the valley opposite Beth-peor.
Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.

< Deuteronomy 3 >