< Colossians 3 >
1 If therefore ye were raised with the Christ, seek the things above, where Christ is, sitting at the right hand of God.
Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah.
2 Think on the things above, not the things on the earth.
Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba.
3 For ye died, and your life has been hidden with the Christ in God.
Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah.
4 When the Christ, our life, is made known, then ye also will be made known with him in glory.
Sa’ad da Kiristi, wanda shi ne ranku, ya bayyana, ku ma za ku bayyana tare da shi cikin ɗaukaka.
5 Put to death therefore your body-parts on the earth: fornication, uncleanness, passion, evil desire, and greed, which is idolatry.
Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne.
6 Because of which the wrath of God comes upon the sons of disobedience,
Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.
7 in which ye also once walked when ye lived in them.
Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali.
8 But now ye also, put off all these things: anger, wrath, wickedness, reviling, filthy speaking out of your mouth.
Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku.
9 Do not lie to each other, having stripped off the old man with his practices,
Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa
10 and having put on the new man, being renewed in knowledge according to an image of him who created him,
kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa.
11 where there is no Greek and Jew, circumcision and uncircumcision, barbarian, Scythian, bondman, freeman, but the all and in all, Christ.
A wannan sabuwar rayuwa babu bambanci ko kai mutumin Al’ummai ne ko mutumin Yahuda, mai kaciya ne ko marar kaciya, baƙo, baƙauye, bawa ne ko’yantacce, gama Kiristi shi ne kome, kuma yana cikin kome.
12 Put on therefore, as chosen men of God, holy and beloved, bowels of compassion, kindness, humility, meekness, longsuffering,
Da yake Allah ya mai da ku zaɓaɓɓu, tsarkaka, ƙaunatattu, sai ku dinga jin tausayin juna, kuna yin alheri, kuna nuna tawali’u da sauƙinkai da jimrewa.
13 forbearing each other, and forgiving yourselves, if any man has a complaint against any, just as also the Christ forgave you, so also ye,
Ku riƙa yin haƙuri da juna kuna kuma gafarta wa juna duk wani laifin da wani ya yi muku. Ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarce ku.
14 and above all these things, love, which is the bond of perfection.
Fiye da waɗannan duka, ku yi ƙaunar juna, gama ƙauna ce take haɗa kome gaba ɗaya.
15 And let the peace of God umpire in your hearts, for which also ye were called in one body, and become thankful.
Ku bar salamar Kiristi tă yi mulki a zukatanku, da yake a matsayin gaɓoɓin jiki ɗaya an kira ku ga salama. Ku zama masu godiya.
16 Let the word of Christ dwell in you abundantly in all wisdom, teaching and admonishing yourselves in psalms and hymns and spiritual songs, singing by grace in your hearts to God.
Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah.
17 And all things, anything whatever ye may do in word or in deed, do all in the name of the Lord Jesus, expressing thanks to the God and Father through him.
Kuma ko mene ne kuke yi, ko cikin magana ko cikin ayyuka, ku yi shi duka a cikin sunan Ubangiji Yesu, kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
18 Wives, be ye submissive to your own husbands as is proper in the Lord.
Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.
19 Husbands, love the wives and do not be made bitter against them.
Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.
20 Children, obey the parents in all things, for this is well-pleasing in the Lord.
’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.
21 Fathers, do not provoke your children, so that they may not be discouraged.
Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.
22 Bondmen, obey in all things those masters according to flesh, not in eye-service as men-pleasers, but in simplicity of heart, fearing God.
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya cikin kome; kada ku yi aikin ganin ido kamar masu neman yabon mutane, sai dai ku yi aiki tsakaninku da Allah, kamar masu tsoron Ubangiji.
23 And all things, anything whatever ye may do, work from soul as to the Lord and not to men,
Kome kuke yi, ku yi shi da dukan zuciyarku, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba ga mutum ba.
24 knowing that from the Lord ye will receive the reward of the inheritance, for ye serve the Lord Christ.
Kun san cewa zai ba ku gādo a matsayin ladanku. Ubangiji Kiristi ne fa kuke bauta wa.
25 And he who does wrong will be recompensed what he did wrong, and there is no partiality.
Duk wanda ya yi laifi, za a sāka masa don laifinsa, babu sonkai.