< Amos 2 >
1 Thus says Jehovah: For three transgressions of Moab, yea, for four, I will not turn away the punishment of it, because he burned the bones of the king of Edom into lime.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
2 But I will send a fire upon Moab, and it shall devour the palaces of Kerioth, and Moab shall die with tumult, with shouting, and with the sound of the trumpet.
Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
3 And I will cut off the judge from the midst of it, and will kill all the rulers of it with him, says Jehovah.
Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
4 Thus says Jehovah: For three transgressions of Judah, yea, for four, I will not turn away the punishment of it, because they have rejected the law of Jehovah, and have not kept his statutes, and their lies have caused them to err, according to which their fathers walked.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
5 But I will send a fire upon Judah, and it shall devour the palaces of Jerusalem.
Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
6 Thus says Jehovah: For three transgressions of Israel, yea, for four, I will not turn away the punishment of it, because they have sold a righteous man for silver, and a needy man for a pair of shoes-
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
7 those who pant after the dust of the earth on the head of the poor, and turn aside the way of the meek. And a man and his father go to the same maiden, to profane my holy name.
Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
8 And they lay themselves down beside every altar upon clothes taken in pledge. And in the house of their God they drink the wine of such as have been fined.
Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
9 Yet I destroyed the Amorite before them, whose height was like the height of the cedars, and he was strong as the oaks, yet I destroyed his fruit from above, and his roots from beneath.
“Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
10 Also I brought you up out of the land of Egypt, and led you forty years in the wilderness, to possess the land of the Amorite.
Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
11 And I raised up of your sons for prophets, and of your young men for Nazirites. Is it not even thus, O ye sons of Israel? says Jehovah.
“Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
12 But ye gave the Nazirites wine to drink, and commanded the prophets, saying, Do not Prophesy.
“Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
13 Behold, I will press you in your place, as a cart presses that is full of sheaves.
“Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
14 And flight shall perish from the swift, and the strong shall not strengthen his force, nor shall the mighty deliver himself.
Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
15 Neither shall he stand who handles the bow. And he who is swift of foot shall not deliver himself, nor shall he who rides the horse deliver himself.
’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
16 And he who is courageous among the mighty shall flee away naked in that day, says Jehovah.
Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.