< Acts 5 >

1 But a certain man named Ananias, with Sapphira his wife, sold property,
Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
2 and kept back from the price, his wife also having joint awareness. And having brought a certain part, he placed it at the apostles' feet.
Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
3 But Peter said, Ananias, why did Satan fill thy heart for thee to lie to the Holy Spirit, and to keep back from the price of the land?
Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
4 While it remained, did it not remain to thee? And after it was sold, it was in thine authority. Why is it that thou have placed this matter in thy heart? Thou have not lied to men, but to God.
Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
5 And Ananias hearing these words, after falling down he expired. And great fear developed in all who heard these things.
Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
6 And after rising the young men wrapped him, and having carried him out they buried him.
Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
7 And it came to pass after an interval of three hours, his wife also came in, not knowing that which happened.
Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
8 And Peter responded to her, Tell me whether ye sold the land for so much. And she said, Yes, for so much.
Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
9 But Peter said to her, How is it that it was agreed by you to challenge the Spirit of the Lord? Behold, the feet of those who buried thy husband are at the door, and they will carry thee out.
Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
10 And immediately she fell down at his feet and expired. And after coming in the young men found her dead, and having carried her out, they buried her by her husband.
Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
11 And great fear developed in the whole church, and in all who heard these things.
Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
12 And by the hands of the apostles many signs and wonders happened among the people. And they were all with one accord in Solomon's porch.
Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
13 But of the rest no man dared join them, but the people magnified them.
Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
14 And more who believe were added to the Lord, multitudes both of men and women,
Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
15 so as to bring the feeble to the thoroughfares, and to place them on cots and mats, so that while coming, the shadow of Peter might at the least overshadow some of them.
har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
16 And also the populace of the cities round about came together to Jerusalem bringing the feeble, and those tormented by unclean spirits, who were all healed.
Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
17 But after rising up, the high priest and all those with him (being the sect of the Sadducees) were filled of envy.
Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
18 And they threw their hands on the apostles, and put them in the public prison.
suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
19 But an agent of the Lord opened the prison doors by night, and after leading them out, he said,
A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
20 Go ye, and after standing in the temple, speak to the people all the sayings of this Life.
“Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
21 And having heard, they entered into the temple at early morning, and taught. But the high priest having arrived, and those with him, they called the council together, and all the senate of the sons of Israel. And they sent to the prison for them to be brought.
Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
22 But the subordinates who came did not find them in the prison. And having returned, they reported,
Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
23 saying, We found the prison indeed shut in all security, and the guards standing before the doors, but after opening, we found no man inside.
Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
24 Now when they heard these words, the high priest, and the captain of the temple, and the chief priests, were perplexed about them, whatever this would become.
Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
25 But a certain man who arrived, reported to them, Behold, the men whom ye put in the prison are standing in the temple and teaching the people.
Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
26 Then after departing, the captain with the subordinates brought them, not with violence, for they feared the people, lest they would be stoned.
Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
27 And having brought them, they placed them in the council. And the high priest demanded them,
Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
28 saying, Did we not command by an order for you not to teach in this name? And behold, ye have filled Jerusalem of your doctrine, and intend to bring upon us this man's blood.
cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
29 And Peter and the apostles having answered, they said, We must obey God rather than men.
Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
30 The God of our fathers raised up Jesus, whom ye murdered, having hung on a tree.
Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
31 God exalted this man with his right hand, a Pathfinder and a Savior to give repentance to Israel and remission of sins.
Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
32 And we are his witnesses of these things, and also the Holy Spirit whom God has given to those who obey him.
Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
33 And when they heard this, they were as being split with a saw, and wanted to annihilate them.
Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
34 But after standing up in the council, a certain Pharisee named Gamaliel, a law teacher, esteemed by all the people, commanded to make the apostles be outside a little while.
Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
35 And he said to them, Men, Israelites, take heed to yourselves what ye are going to do against these men.
Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
36 For before these days Theudas rose up saying himself to be somebody, to whom a number of men, about four hundred, bonded themselves, who was killed. And all, as many as were persuaded by him, were dispersed and developed into nothing.
A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
37 After this man Judas the Galilean rose up in the days of the registration, and drew a considerable crowd behind him. That man was also destroyed, and all, as many as were persuaded by him, were scattered.
Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
38 And now I say to you, keep away from these men, and let them go, because if the project or this work is from men, it will be overthrown,
Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
39 but if it is from God, ye cannot overthrow it, and perhaps ye may be found to be fighting against God.
Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
40 And they were persuaded by him. And after summoning the apostles, having beat them, they commanded them not to speak in the name of Jesus, and released them.
Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
41 Indeed therefore they departed from the presence of the council, rejoicing that they were considered worthy to be treated shamefully for the name of Jesus.
Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
42 And every day, in the temple and from house to house, they ceased not teaching and preaching good news, Jesus, the Christ.
Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.

< Acts 5 >